Hukumar 'Yan Sandan Najeriya Ta Karyata Sanarwar Janye Jami'anta Daga 'Yan siyasa

Hukumar 'Yan Sandan Najeriya Ta Karyata Sanarwar Janye Jami'anta Daga 'Yan siyasa

  • Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ce labarin janye jami'an tsaro daga 'yan siyasa da aka ce ta yi ba gaskiya ba ne
  • Rundunar ta kuma ce takardar da aka yaɗa musamman a kafafen sada zumunta ta bogi ce ba ta gaskiya ba
  • Hukumar ta kuma yi kira ga 'yan Najeriya da su kasance masu lura sosai wajen tantance labaran gaskiya da na bogi

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta musanta labarin da ake yaɗawa na cewa ta janye jami'anta dake bai wa ‘yan siyasa kariya.

Jami'in hulɗa da jama'a na 'yan sandan Najeriya, CSP Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan ta shafin rundunar na Tuwita.

Rundunar 'yan sandan Najeriya ta karyata labarin janye jami'an tsaro
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta musanta batun janye jami'anta daga 'yan siyasa. Hoto: @princemoye1
Asali: Twitter

'Yan sanda sun ce takardar ta bogi ce

Ya ce takardar wacce aka yaɗa mai ɗauke da umarnin cewa an janye jami'an ‘yan sanda daga wasu manyan ‘yan siyasa da ‘yan uwansu ta bogi ce.

Kara karanta wannan

Subhanallahi: An Tabbatar Da Bullar Cutar Nan Mai Kisa Wacce Ake Kira 'Anthrax' a Najeriya

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Ya ƙara da cewa, takarda ta saɓa da ƙa'idar yadda suke fitar da saƙonninsu domin kuwa tana ɗauke da sanya hannun da ba shi ne ya dace ba.

Da yake mayar da martani kan batun, Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, PhD, NPM, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan inda aka samu takardar ta bogi.

An shawarci 'yan Najeriya su riƙa tantance labaran da suke yaɗawa

Egbetokun ya kuma ba da tabbacin cewa, za a ɗauki matakin da ya dace a kan waɗanda suka ƙirƙiro ƙaryar da kuma yaɗa ta.

Wannan bayanin dai zai kwantar da hankalin 'yan siyasa da 'yan uwansu da suka ɗaga hankalinsu dangane da labarin ƙaryar da aka yaɗa kamar yadda Nigerian Tribune ta wallafa.

Rundunar 'yan sandan ta kirayi 'yan Najeriya da su riƙa sanya idanu sosai wajen tantance labaran gaskiya da na ƙarya, musamman ma wanda ake ɗorawa a a kafafen sada zumunta.

Kara karanta wannan

Peter Obi Ya Bayyana Gaskiya Kan Batun Sake Tsayawa Takarar Shugaban Kasa a Shekarar 2027

'Yan sanda sun kama masu garkuwa da mutane bakwai a Bauchi

Legit.ng a baya ta kawo muku rahoto cewa , jami'an hukumar 'yan sanda reshen jihar Bauchi, sun yi nasarar cafke wasu mutane bakwai da ake zarginsu da garkuwa da mutane.

An bayyana cewa an kama mutanen ne a yankin alƙaleri da ke jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng