Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi da Kai Wa Ayarin Babban Malami Hari

Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi da Kai Wa Ayarin Babban Malami Hari

  • Dakarun yan sanda sun samu nasarar kama wanda ake zargi da hannu a harin da aka kai wa fitaccen malamin coci, Apostle Johnson Suleman
  • Mai magana da yawun hukumar 'yan sandan kasar nan, Muyiwa Adejobi, ya ce jami'ai sun kwato manyan bindigu daga hannunsa
  • Mutumin mai suna Yusuf Isah ya shiga hannun jami'an yan sanda na sashin tattara bayanan sirri bayan gudanar da bincike mai zurfi

FCT Abuja - Hukumar 'yan sandan Najeriya ta kama wani mutumi ɗan shekara 32 a duniya mai suna, Yusuf Isah, bisa zargin yana da hannu a harin da aka kai wa babban Malamin coci.

Jaridar Punch ta rahoto cewa mutumin ya shiga hannu ne kan zargin alaƙa da kazamin harin da aka kai wa babban Fasto kuma shugaban mabiya Omega Fire Ministries na duniya, Johnson Suleman.

Kara karanta wannan

Nasara: Gwamnan APC Ya Yi Abu 1, Ya Ceto Mutane 30 Na Jihohin Arewa 3 Daga Hannun 'Yan Bindiga

Wanda ake zargi da hannu a kai hari kan ayarin Fasto Johnson Suleman.
Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi da Kai Wa Ayarin Babban Malami Hari Hoto: punchng
Asali: UGC

Yadda mummunan harin ya faru

Idan baku manta ba a watan Oktoba, 2022, wasu miyagun 'yan bindiga suka farmaki ayarin motocin fitaccen Faston a kan titin Benin-Auchi cikin jihar Edo.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Yayin wannan hari, 'yan bindigan sun halaka mutane shida kuma daga cikinsu harda jami'an hukumar 'yan sanda guda uku.

Yadda muka kama wanda ake zargi - hukumar 'yan sanda

Jami'in hulɗa da jama'a na hukumar 'yan sandan Najeriya, Muyiwa Adejobi, ya tabbatar da kama Yusuf Isa ga 'yan jarida a birnin tarayya Abuja.

Da yake jawabi yayin nuna wanda ake zargin, Adejobi ya ce jami'an sashin tattara bayanan sirri (FIB-IRT) ne suka kama Isah bayan gudanar da bincike mai zurfi.

Ya ce yan sanda sun kwato bindigun AK-47 guda 5, bindigun K2 guda biyu da alburusai 180 daga hannun wanda ake zargi, kamar yadda Vanguard ta rahoto.

Kara karanta wannan

Yadda Hoton Rahama Sadau Da Wani Farin Fata Ya Haddasa Cece-Kuce a Soshiyal Midiya

"Bayan bincike mai zurfi dangane da harin da aka kai wa ayarin Fasto, Apostle Johnson Suleman, jami'an sashin FIB-IRT sun kama Yusuf Isah ɗan asalin garin Okene, jihar Kogi kuma yana sana'a a Akure, jihar Ondo."
"An samun bindigun Ak47 guda biyar, bindiga ƙirar K2 guda biyu, alburusai guda 180 da kuma wasu abubuwan fashewa 4 a gidan da yake zama."

- Muyiwa Adejobi.

Gwamnatin Kebbi Ta Kubutar da Mutane 30 Daga Hannun 'Yan Bindiga

A wani labarin kuma Gwamnatin jihar Kebbi da ke Arewa maso Yammacin Najeriya ta ceto mutum 30 da suka fito daga jihohi 3 daga hannun 'yan bindiga.

Shugaban ƙaramar hukumar Danko-Wasagu, Honorabul Hussaini Aliyu Bena, shi ne ya bayyana haka ga 'yan jarida a Birnin Kebbi ranar Laraba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262