Shugaban Ma’aikatan Tsaro: Abubuwa 7 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Manjo Janar C.G Musa

Shugaban Ma’aikatan Tsaro: Abubuwa 7 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Manjo Janar C.G Musa

Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya nada Manjo Janar Christopher Gwabin Musa a matsayin sabon shugaban ma'aikatan tsaro don maye gurbin Janar Lucky Irabor.

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Shugaban kasa Tinubu ya amince da yi wa shugabannin tsaro ritaya nan take sannan ya sanar da madadinsu.

Shugaban ma'aikatan tsaro
Shugaban Ma’aikatan Tsaro: Abubuwa 7 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Janar C.G Musa Hoto: Kogi Sultan/ BJ Bulama
Asali: Facebook

Legit.ng ta tattaro muhimman abubuwa game da sabon shugaban ma'aikatan tsaron.

Ranar haihuwarsa

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa an haifi Musa a ranar 25 ga watan Disambar 1967 a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Jiharsa

Ya kasance dan arewa Kirista daga karamar hukumar Zangon Kataf da ke kudancin jihar Kaduna.

Karatu

Musa ya yi karatunsa na firamare da sakandare a jihar Sokoto.

Kara karanta wannan

Janar Taoreed Abiodun Lagbaja: Abubuwa 6 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban Hafsan Sojoji

Ya yi Difloma a faddin tsaro daga jami'ar Lagas, Difloma a bangaren dabarun tsaro a China da sauransu.

Shiga soja

Musa ya samu shiga makarantar sojoji ta NDA Kaduna a 1986 inda ya samu horo na tsawon shekaru biyar.

Laftanal na biyu a rundunar sojojin kasa

A watan Satumban 1991 ya shiga aikin sojan Najeriya a matsayin laftanar na biyu a rundunar sojojin, daya daga cikin sashi mafi wahala a rundunar soji.

Kwamandan bataliyar tsaron runduna ta 73

Ya kasance babban jami'in horarwa/ayyuka sashi na 81, hedkwata, ya kasance babban kwamandan Bataliya ta 73, Mataimakin Daraktan Ayyuka a Sashen Tsare-tsare na rundunar sojoji.

Kwamandan Sashi na 3 OP LAFIYA DOLE

Musa kasance kwamandan sashi na 3 OP LAFIYA DOLE, Kwamandan Sashe na 3 na rundunar hadin gwiwa a yankin tafkin Tchad, ya kuma rike mukamai da dama da ba a ambace su ba, PM News ta rahoto.

Kara karanta wannan

Shugaban Kasa Bola Tinubu: Cikakkun Sunayen Hafsoshin Tsaro, Manyan Kwamandojin Fadar Shugaban Kasa Da Sauransu

A 2021, ya kuma rike shugabancin Operation Hadin Kai da ke yaki da yan ta’adda a Arewa maso gabas.

Sabon shugaban hafsan soji: Abubuwan da ya kamata ku sani game da Janar Lagbaja

A wani labarin, Legit.ng ta kawo a baya cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana Janar Taoreed Abiodun Lagbaja a matsayin sabon shugaban hafsan sojojin Najeriya a ranar Litinin, 19 ga watan Yuni..

Ana ganin Janar Lagbaja na daya daga cikin janarori da suka san kan aiki sosai a rundunar sojojin Najeriya.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel