Yan Bindiga Sun Halaka Manoma 2 A Gonakinsu Jihar Ƙaduna

Yan Bindiga Sun Halaka Manoma 2 A Gonakinsu Jihar Ƙaduna

  • Ƴan bindiga sun sake kai hari a yankin Birnin Gwari inda suka halaka wasu manoma mutum biyu a gonakinsu
  • Ƴan bindigan sun halaka manoman ne a yayin da su ke tsaka da aiki a gonakinsu ranar Juma'a a ƙauyen Unguwar Gajere
  • A ranar Alhamis ƴan bindigan sun kuma yi awon gaba da wasu manoman guda biyu a ƙauyen Gwanda mai Gyada

Jihar Kaduna - Ƴan bindiga sun halaka. wasu ƴan uwan juna suna tsaka da noma a ƙauyen Unguwar Gajere, cikin mazaɓar Kutemeshi, a ƙaramar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna.

Jaridar Daily Trust ta kawo rahoto cewa lamarin ya auku ne a ranar Juma'a da safe lokacin da mutanen su ke aiki a gonakinsu.

'Yan bindiga sun halaka manoma a jihar Kaduna
Yan bindigan sun halaka manoman a gonakinsu Hoto: Punch.com
Asali: UGC

Sagir Umar, wani mazaunin yankin ya nuna damuwarsa kan yadda ƴan bindiga ke cin karensu babu babbaka a yankin, wanda hakan ya tada hankulan mutanen ƙauyen.

Kara karanta wannan

Gaskiya Ta Bayyana Kan Dalilin Da Ya Sanya 'Yan Majalisun Jam'iyyun Adawa Suka Zabi Abbas Tajudeen

Ƴan bindiga sun addabi yankin da hare-hare

Ya bayyana cewa a cikin sati biyu da suka gabata, aƙalla mutanen ƙauyen mutum 10 ƴan bindiga suka riƙe a hannunsu.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

A cewar Umar, ƴan bindigan sun addabi mutanen ƙauyen ta hanyar yi musu ɗauki ɗai-ɗai da sace musu dabbobi.

Yahaya Musa, ɗan majalisar dokokin jihar Kaduna mai wakiltar Kakangi, ya tabbatar da aukuwar kisan na kwanan nan sannan ya nuna takaicinsa kan lamarin.

Ya kuma ƙara bayyana cewa ƴan bindigan sun kuma sace wasu manoman guda biyu a ƙauyen Gwanda mai Gyada, a ranar Alhamis suna cikin aiki a gonakinsu.

Lokacin da aka tuntuɓi kakakin rundunar ƴan sandan jihar domin jin ta bakinsa, DSP Mohammed Jalige, ya yi alƙawarin zai sake kiran wakilin majiyarmu domin bayar da cikakken bayani kan lamarin.

Sai dai, har ya zuwa lokacin kammala haɗa wannan rahoton ba sake jin ɗuriyarsa ba.

Kara karanta wannan

Gwara Haka: A Kokarin Tserewa Sojoji Mai Garkuwa Da Mutane Ya Sheka Barzahu

'Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Malamin Coci a Jihar Benue

A wani labarin na daban kuma, ƴan bindiga sun sace wani malamin cocin Otukpo Diocese, Rabaran Anthony Adikwu

Malamin Cocin da miyagun suka yi garkuwa da shi yana aiki a cocin St. Margaret’s Parish da ke garin Ajegbe Awume, ƙaramar hukumar Ohimini ta jihar Benue.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng