Da So Samu Ne, a Samu Jirage 4 Su Yi Zuwa Daya Su Kwaso ’Yan Najeriya Daga Sudan Kowa Ya Huta
- Gwamnatin Najeriya ta ce akwai bukatar karin jirage hudu domin kwaso ‘yan Najeriyan da suka makale a Sudan
- Ana ci gaba da tattaro ‘yan Najeriyan da yaki ya rutsa dasu a Sudan, inda da yawa suka yi hijira zuwa Masar
- A jiya, an tattaro mutum 350 da aka ce sun galabaita a kasar, inda suka samu kyautar kudi daga gwamnati
FCT, Abuja - Gwamnaton Najeriya ta ce, idan da za a samu jiragen sama hudu, zuwa daya za a yi wajen kwaso dukkan daliban da suka makale a kasar Sudan da ke fama da rikici.
Rukunin farko na ‘yan Najeriyan da suka makale a Sudan tuni aka dauko su a jiya Laraba, inda aka sauke su a filin saukar jiragen sama da ke Abuja, Vanguard ta ruwaito.

Kara karanta wannan
Gobarar titi: Gwamnati ta raba wa wadanda aka kwaso daga Sudan N100k, katin N25k da data 1.5GB
A cewar hukumomin Najeriya, shirin tattaro ‘yan Najeriya da ke kasar zai kai mutum 3,500, amma akwai yiwuwar sun fi haka gidan aka hada da dalibai da wadanda ke rayuwa a can.

Asali: Twitter
Jirgin kasuwanci na Najeriya, Air Peace ya sauka a jiya da misalin karfe 11:40 na dare dauke da mutane 260, yayin da jirgin sojin sama kuma ya dauko mutum 94.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Da so samu ne, a samu karin jirage 4 su kwaso ‘yan Najeriya daga Sudan
A bangare guda, shugaban hukumar kula da ‘yan Najeriya mazauna waje (NiDCOM), Abike Dabiri Erewa ta ce da za a samu karin jirage hudu da an rage aiki.
A cewarta, idan akwai karin jirage hudu, zuwa daya za a yi wajen kwaso ‘yan Najeriyan da suka makale a kasar ta Sudan, rahoton Punch.
Ta bayyana hakan ne a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja yayin da ake jiran saukar ‘yan Najeriyan da aka dauko daga Masar.

Kara karanta wannan
Gwamnatin Buhari Ta Faɗi Matsalar da Aka Samu Da halin da Ragowar 'Yan Najeriya Ke Ciki a Sudan
A cewarta, a yanzu haka, ana tsammanin kwaso ‘yan Najeriyan da suka makale akalla 3,000.
Ta kuma shaida cewa, gwamnatin Masar na ci gaba da nuna bukatar a turo jirage domin kwashe ‘yan Najeriya da ke cikin kasar wadanda suka yi hijira daga Sudan.
An raba wa ‘yan Najeriyan da aka kwaso daga Sudan kudi
A bangare guda, rahoto ya bayyana yadda aka raba wa ‘yan Najeriyan da aka kwaso daga Sudan kudi a filin jirgin Najeriya.
Kudin na zuwa ne ta ma’aikatar jin kai da walwala, inda aka ce Dangote ne ya ba da kudin a basu.
Hakazalika, an ce kamfanin MTN ya ba ‘yan Najeriya katin waya na N25,000 da kuma data 1.5GB duk dai a lokacin da suka sauka a kasar.
Asali: Legit.ng