Kotu Ta Soke Tarukan Jam’iyyar APC Na Kogi Na Zabo Dan Takarar Gwamna

Kotu Ta Soke Tarukan Jam’iyyar APC Na Kogi Na Zabo Dan Takarar Gwamna

  • Kotu ta soke zabukan da aka yi na samar da dan takarar gwamnan APC a jihar Kogi saboda wasu dalilai
  • Wannan na faru ne bayan da wasu jiga-jigan jam'iyyar suka maka wadanda suka gudanar da tarukan zaben a kotu
  • Ya zuwa, kotun ta umarci APC ta gudanar da sahihin taron zabe daidai da kundin zabe da kundin mulkin APC

FCT, Abuja - Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta soke tarukan gundumomi da na kananan hukumomi da aka ce jam’iyyar APC ta gudanar a ranar 7 ga watan Fabrairu a Kogi domin samar da dan takararta a zaben gwamna da za a yi a watan Nuwamba.

A tun farko, wasu mambobin jam’iyyar APC a karkashin jagorancin Realwan Okpanachi sun garzaya kotu domin neman a soke zabukan biyu da aka gudanar a jihar, Tribune Online ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Ka kama kanka: Dattawan Arewa sun ce Peter Obi na son tada hankali a Najeriiya

Da yake yanke hukunci a ranar Laraba, Mai shari’a James Omotosho ya haramtawa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) yin amfani da jerin sunayen deleget-deleget da jam’iyyar ta fitar daga tarukan don tsayar da dan takarar gwamna.

An soke tarukan APC an Kogi
Jihar Kogi da ke Arewa ta Tsakiya | Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

Dalilin soke taron da aka yi

Kotun ta soke tarukan ne saboda ba a gudanar da su daidai da yadda dokar zabe ta 2022 da kuma kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC suka tanada ba.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Hakazalika mai shari’a Omotosho ya bayyana cewa jam’iyyar APC ta kasa fitar da takardar sakamakon zaben domin nuna adadin kuri'un da mahalarta taron sun kada a gundumomi da kananan hukumomin.

Ba wannan ne karon farko da ake samun matsalar da ke kai wa ga soke zaben fidda gwani ko shirinsa ba a Najeriya, Channels Tv ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Ku rabu dashi: Peter Obi ya tafi kotu ya shirga karya game da zabe, INEC ta yi martani

Don haka kotun ta umurci jam’iyyar APC da ta gudanar da taro na musamman na gunduma da kananan hukumomi bisa tanadin dokokin da suka dace, musamman sashe na 84 na dokar zabe da sashe na 13 na kundin tsarin mulkin APC.

A baya kun ji yadda majalisar dokokin jihar Kano ta amince da bukatar gwamna Abdullahi Umar Ganduje na gyara ga masarautun jihar Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.