Wasu ’Yan Bindiga Sun Kashe ASP Tare da Raunata Wasu Jami’ai a Shingen Bincike a Legas
- An kashe wani dan sanda tare da jikkata wasu jami’ai da yawa a wnai yankin jihar Legas da ke Kudu maso Yamma
- Wannan ya faru ne bayan da wasu ‘yan ta’adda suka hallaka ‘yan sanda a wata unguwa da ke jihar ta Legas
- ‘Yan sanda sun tabbatar da faruwar lamarin, sun bayyana matakin da suke dauka a halin da ake ciki
Jihar Legas - Wasu tsagerun ‘yan bindiga sun sheke ASP na ‘yan sanda tare da jikkata wasi jami’ai a wani farmakin da suka kai kan tirken binciken jami’an da ke Ikorodu a jihar Legas.
An kuma ruwaito cewa, ‘yan ta’addan sun tsere da bindigogi biyu na ‘yan sandan da aka ce sun tsaya a magamar Enure da ke Itokin a kusa da babban titin Ikorodu zuwa Abeokuta.
An tattaro cewa, lamarin ya faru ne a daren Juma’a, kasa awanni 48 kenan bayan da ‘yan bindigan kashe mazauna uku na unguwar Gowon da ke Ipaja kana kasa da awanni 24 da hallaka ‘yan sanda uku a wani yankin jihar Edo.

Asali: UGC
Yadda lamarin ya faru
Majiya ta shaidawa jaridar The Nation cewa, ana zargin wasu matsafa ne suka kai harin, wadanda aka ce sun dauki lokaci suna barna a yankin na Legas.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Hakazalika, an gano cewa, akalla mutane hudu wadannan matsafa suka kashe a yankin Ikorodu, inda aka ce suna aiki ne ga wani mai kwace filayen jama’a.
Wata majiyar da ta nemi a sakaya sunanta ta ce:
“Matsafan na nan a Emuren kuma sun yi kaurin suna. Suna yiwa wani fitaccen mai kwace filayen jama’a aiki ne a Ikorodu.”
Maranin ‘yan sanda
A lokacin da aka tuntube shi, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin ya tabbatar da faruwar lamarin, inda yace ana ci gaba da bincike a kai.
A cewarsa, ba za a bayyana sunaye da bayanan ‘yan sandan da suka mutu ba sai har an sanar da ahalinsu yadda ya dace.

Kara karanta wannan
Dubu ta cika: Kasurgumin fursunan da ya tsere a magarkamar Kuje ya sake shiga hannu
Ya kuma tabbatar da cewa, an kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannun a kisan da aka yi a unguwar Gowon a ranar Laraba da dare.
Ya kara da cewa, an kama wadanda ake zargin ne a ranar Alhamis, kuma sun tabbatar da suna da hannu a barnar da ta auku.
A jihar Bauchi kuma an kama wasu matasa da ake zargin ‘yan daba ne da suka addabi jama’a a jihar.
Asali: Legit.ng