Masu Zanga-Zanga Na Neman Shugaban INEC Yayi Murabus Daga Kujerar Sa

Masu Zanga-Zanga Na Neman Shugaban INEC Yayi Murabus Daga Kujerar Sa

  • Masu zanga-zanga sun taso shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa a gaba kan sai yayi murabus
  • Masu zanga-zangar na neman farfasa Mahmood Yakubu yayi murabus daga kujerar sa kan rikicin da aka samu lokacim zaɓe
  • A cewar su a lokacin zaɓen an tauye haƙƙin ƴan Najeriya da dama ta hanyar hana su kaɗa ƙuri'un su

Abuja- Masu zanga-zanga daga jihohi daban-daban na tarayyar Najeriya a ranar Alhamis sun dira birnin tarayya Abuja suna neman shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) yayi murabus.

Masu zanga-zangar suna neman farfesa Mahmood Yakubu yayi murabus daga kan muƙamin sa saboda rikicin da aka samu a zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisun tarayya a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023. Rahoton Daily Trust

Yakubu
Masu Zanga-Zanga Na Neman Shugaban INEC Yayi Murabus Daga Kujerar Sa
Source: Original

Idan ba a manta ba dai an samu rikici, kwacen takardun kaɗa ƙuri'a da akwatunan zaɓe, da harbe-harbe a wasu jihohi a lokacin zaɓen.

Kara karanta wannan

“Karku Rantsar da Tinubu Domin Yin Hakan Ya Sabawa Dokar Tsarin Mulkin Najeriya” - Baba Ahmed

Shugaban masu zanga-zangar, Anngu Orngu, yace wasu matasa da suka fito a karon su na farko domin kaɗa ƙuri'un su, an hana su yin zaɓen a dalilin rikicin da ya auku a zaɓen.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

A kalamansa:

“Mu ƴan Najeriya ne mara sa son tashin hankali, amma zamu yi amfani da duk hanyar da ta dace bisa doka wajen ganin cewa an biya mana buƙatun mu."
"Mun taru a nan ne cikin takaici domin an tattaka ƴancin da ƴan Najeriya suke da shi, sannan mun taru a nan ne domin yin kira kan yin murabus ɗin shugaban hukumar INEC, farfesa Mahmood Yakubu da gaggawa."

Wani jagoran zanga-zangar a ƙarƙashin ƙungiyar National Youth League for the Defence of Democracy (NYLDD), Dr Moses Paul, ya bayyana cewa:

“An ƙona mutane a Kano, an harbi mutane a Rivers, mun ga rashin imanin da aka yi a jihar Legas duk a lokacin zaɓen nan."

Jaridar Tribune ta rahoto cewa masu zanga-zangar na kuma neman shugaba Buhari da ya kafa gwamnatin riƙon ƙwarya kafin ƙarewar wa'adin mulkin sa.

Kara karanta wannan

Sa'o'i Kadan Bayan Ya Lashe Zabe, Zababben Gwamna Yayi Jawabi Mai Ratsa Zuciya

Kotun Daukaka Kara Zata Zartar Da Hukunci Kan Shari'ar Gwamnan Jihar Osun

A wani labarin na daban kuma, kotun ɗaukaka ƙara ta shirya zartar da hukuncin ta kan sahihin gwamnan jihar Osun.

Kotun ɗaukaka ƙarar za ta yi hukuncin ta ne a yau.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng