Tsohon Gwamna Oshiomhole Ya Lashe Zaben Sanatan Edo Ta Arewa
- Tsohon shugaban jam'iyyar APC na kasa ya lashe zaben sanata a mazabar Edo ta Arewa a Kudancin Najeriya
- Adams Oshiomole ya samu kuri'u da yawa, inda ya banke abokan hamayyarsa a jam'iyyar PDP da sauran jam'iyyu
- Ana ci gaba da fito da sakamakon zabe a yankuna daban-daban na Najeriya tun bayan kammala zabe a ranar Asabar
Jihar Edo - Adams Oshiomole, tsohon gwamnan jihar Edo kuma tsohon shugaban jam'iyyar APC na kasa ya lashe kujerar sanata a Edo ta Arewa
Oshionole ya samu kuri'u 107,110, inda ya banke abokin hamayyarsa Francis Alimikhena na jam'iyyar PDP, Sahara Reporters ta tattaro.
Alimikhena ya samu kuri'u 55,344.

Asali: UGC
Hukumar INEC ta sanar da Oshiomole ne ya lashe zabe
Benjamin Adesina, baturen zabe a jihar Edo ya sanar da cewa, dan takarar da ya lashe zabe a mazabar Edo ta Arewa dai ba kowa bane face Oshiomole.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A cewarsa:
“Adams Oshiomole na APC, ya samu kuri'u mafi rinjaye a zaben, don haka shi ne dan takarar da ya lashe zaben da aka yi a ranar 25 ga watan Faburairu a mazabar sanata ta Edo ta Arewa.
Adams Oshiomole ya kasance daya daga cikin masu fada a ji a jam'iyyar APC mai mulki, kuma ya yi gwamna a Edo a shekarun baya da suka shude.
A lokacin da yake shugaban APC ne aka kafa gwamnatin Buhari, kuma tasirinsa ya shafi bangarori daban-daban na siyasar jam'iyyar.
Sanata Bala Ibn Na'Allah ya rasa kujerarsa ta sanata
A wani labarin kuma, jigon APC mai fada a ji ya rasa damar zama sanata a zaben 2023 na 'yan majalisun tarayya da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata 25 ga watan Faburairu.
Rahoton da muka samo ya bayyana cewa, dan takarar sanata a PDP ne ya yi nasarar karbe kujerar a hannun Sanata Bala, wanda ya dade yana rike da ita.

Kara karanta wannan
Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Lashe Zabe a Jihar Oyo, Ya Doke Atiku Da Kuri’u Masu Yawan Gaske
A cewar rahoton, Bala ya kasance sanata har sau biyu a mazabarsa da ke Kebbi, inda kuma ya kasance dan majalisar wakilai a matakin tarayya na tsawon zango biyu a jihar ta Kebbi.
Asali: Legit.ng