Babbar Magana Yayin Daka Nemi Tambarin Jam’iyyar Labour a Jikin Kuri’ar Zaben Ondo Aka Rasa

Babbar Magana Yayin Daka Nemi Tambarin Jam’iyyar Labour a Jikin Kuri’ar Zaben Ondo Aka Rasa

  • An shiga tsaiko da tashin hankali yayin da jam'iyyar Labour ta gaza ganin tambarinta a takardun kuri'u na jihar Ondo
  • Wannan lamari ya zo da tsaiko, mambobin jam'iyyar sun bukaci a dage zaben da za a yi a jihar a gobe Asabar
  • Jam'iyyun siyasa da hukumar zabe gaba daya sun bayyana tsayawarsu da shiri a zaben 2023 kafin zuwan wannan tsaikon

Jihar Ondo - Jam'iyyar Labour ta shiga damuwa tare da yin magana bayan da aka nemi tambarinta aka rasa a jikin takardar kuri'a ta zaben gobe Asabar a jihar Ondo, Vaguard ta ruwaito.

Mambobin jam'iyyar Labour da yawa ne suka mamaye ofishin hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ke Alagbaka don nuna adawarsu ga rashin jam'iyyarsu a kuri'un.

Takardun kuri'un, a cewar mambobin Labour na zaben da aka tsara yi ne na 'yan majalisun tarayya a gobe Asabar.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Saura Yan Awanni Zabe, Jam'iyyar APC Ta Dakatar Da Sanata Orji Uzor Kalu

Jam'iyyar Labour ta shiga mamaki bayan ganin babu ita a jerin jam'iyyun bana a jihar Ondo
Jam'iyyar Labour (LP) | Hoto: punchng.com
Asali: UGC

Mazabun da ba a ga tambarin Labour ba

Daily Trust ta tattaro cewa, ba a tambarin jam'iyyar Labour din ba a kuri'un mazabar sanata ta tsakiya a Ondo, Akoko ta Arewa masu Yamma/Arewa maso Gabas da Akoko ta Kudu maso Yamma/Kudu maso Gabas.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakazalika, da na mazabar Akure ta Arewa/Kudu, Okitipupa/Irele, Ilaje/Ese-Odo da kuma Ondo ta Gabas/Yamma.

Ana son take hakkinmu ne

Daya daga cikin 'yan takarar jam'iyyar Labour ya zanta da jaridar, ina ya zargi INEC da cire jam'iyyar da gangan.

A cewarsa:

"Yanzu muka gano cewa takardun kuri'u da aka tura na zaben Sanata da 'yan majalisun tarayya a mazabar Ondo babu tambarin jam'iyyarmu (LP).
"Ina tunanin an shirya take hakkinmu ne a zaben gobe (Asabar). Wannan ba zai yiwu ba. Irin haka ya faru a Legas."

Kara karanta wannan

Saura Kwana 2 Zabe, Yan Daba Sun Bude Wa Shugaban Majalisar Dokoki Wuta Yana Tsaka da Taro

Da yawan mambobin jam'iyyar LP a jihar sun bukaci INEC da ta dage zaben da za a yi gobe a jihar.

Ya zuwa lokacin hada wannan rahoton, ba a samu jin ta bakin mai magana da yawun hukumar zabe mai zaman kanta ba.

Ana ci gaba da fuskatar matsaloli na siyasa a lokacin da zaben ke kara shigowa, an farmaki tawagar matar dan takarar PDP a Zamfara.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.