'Diyar Ganduje Ta Ce Zata Mayar Da Kudin Sadaki N50,000 ga Mijinta a Raba su

'Diyar Ganduje Ta Ce Zata Mayar Da Kudin Sadaki N50,000 ga Mijinta a Raba su

  • Ana cigaba da zaman shari'a tsakanin Hajiya Asiya Ganduje da mijinta Alhaji Inuwa Uba a jihar Kano
  • Asiya Ganduje na bukatar kotu ta raba aurenta da Uba Inuwa saboda wasu dalilai na ta
  • Shi kuwa mijin ya kindaya wasu sharruda da ya wajaba ta cika masa kafin ya amince a raba auren

Kano - Asiya Ganduje, diyar gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ta sake jaddadawa kotu bukatar a raba aurenta na tsawon shekaru 16 da Alhaji Inuwa Uba.

Asiya, a ranar Alhamis ta bayyanawa kotun Shari'ar Musulunci dake Kano cewa shirye take ta mayarwa mijin da N50,000 kudin sadakin da ya biya kanta.

Ta bayyana cewa tana neman khul'i a kotun ne saboda ta gaji da zama da mijinta Inuwa kuma a kawo karshen auren, rahoton Vanguard.

Kara karanta wannan

Kada ku sake kara wa'adin daina amfani da Naira, Atiku ga CBN

Asiya
'Diyar Ganduje Ta Ce Zata Mayar Da Kudin Sadaki N50,000 ga Mijinta a Raba su# Hoto: Vanguard
Asali: Facebook

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

A zaman ranar Alhamis, lauyan Asiya, Ibrahim Aliyu-Nassarawa, ya laburtawa kotu cewa shirya Asiya take da mayarwa mijin kudin sadakin da ya biya N50,000 kanta don ya sake ta.

Yace:

"Kowace mace dake zaman gidan auren da bata jin dadi na da hakki karkashin shari'ar Musulunci ta garzaya kotu neman a raba auren da sharadin za ta mayar da kudin sadaki."
"Wacce nike tsayawa shirye take ta mayar da N50,000 da mijin ya biya sadaki don a raba auren."

Ibrahim Aliyu-Nassarawa ya kara da cewa ta shirya hakuri da dukkan wani hakki na ta amma dai ba zata bi sharrudan da mijin ke kokarin kakaba mata ba, rahoton ya kara.

A cewarsa:

"Sharrudan da ya gindaya abu ne na rikici saboda haka ya kamata ayi zama na musamman a wani kotun."

Kara karanta wannan

Borno: ISWAP Sun Yi Rabon Tsofaffin Kudi ga Fasinjojin Motocin Haya Kyauta, Sun ce SU je Bankuna Su Canza su

Shi kuwa lauyan mijin, Umar I. Umar, ya ce matsalarsu ba kudin sadakin N50,000 bane.

A cewarsa:

"Wanda nike wakilta na da sharruda biyu game da wasu dukiyoyinsa, kafin a zo maganasr rabuwar aure."
"Akwai 'yaya hudu da ta haifa masa amma duk yunkurin sulhun da aka yi ya ci tura."
"Idan tana son a raba auren ta dawo da dukkan takardunsa, takardun gidajensa, motoci, da hannun jarin da take da shi a kamfanin shinkafarsu."
Alkali mai shari'a, Malam Halliru Abdullahi, bayan sauraron jawabansu ya dake zaman zuwa ranar 2 ga watan Febrairu, 2023 don yanke hukunci.

Asali: Legit.ng

Online view pixel