Buhari Zai Karrama Sarkin Kano, Sarkin Zazzau Da Wasu Sarakuna 18 Da Lambar Girma Ta Kasa

Buhari Zai Karrama Sarkin Kano, Sarkin Zazzau Da Wasu Sarakuna 18 Da Lambar Girma Ta Kasa

  • Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai karrama mutane fiye da 400 da lambar girmamawa ta kasa na 2022
  • Daga cikin wadanda za a girmama akwai manyan jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya, manyan masu fada aji da sauransu
  • Sai dai kuma, sarakuna 20 ne suka kai matakin karshe inda Ooni na Ife, da sarkin Kano ke kan gaba a rukunin

An saki jerin sunayen mutanen da gwamnatin Najeriya za ta karrama da lambar girmamawa ta kasa na wannan shekarar.

Legit.ng ta rahoto cewa mutane 437 ne za su samu lambar yabo daga bangarori daban-daban na rayuwa kama daga yan siyasa, yan kasuwa, jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya da kuma masu nishadantarwa.

Sarakuna
Buhari Zai Karrama Sarkin Kano, Sarkin Zazzau Da Wasu Sarakuna 18 Da Lambar Girma Ta Kasa Hoto: Ooni of Ife, Emir of Kano, Olu of Warri, Oba of Benin
Source: UGC

Lambar yabon wannan shekarar ya hada da GCON biyar, CFR 54, CON 67, OFR 64, OON 101, MFR 75, MON 56 da FRM 8.

Kara karanta wannan

Buhari zai karrama Abba Kyari, Tunde, Okonjo-Iweala da Wasu 437 da Lambar Girma

Shugaba Buhari zai gabatarwa kowani mutum da nasa kason lambar girmamawan a fadar shugaban kasa a ranar Talata, 11 ga watan Oktoba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A wannen zauren, Legit.ng ta lissafo wasu daga cikin sarakunan da suka samu shiga sahun wadanda za a karrama a wannan shekarar inda su 20 zasu samu lambar yabo ta CFR.

Ga jerin sunayen sarakunan da aka lissafa za a karrama a kasa:

SUNA

MATSAYI

JIHA

LAMBAR YABO

1

Mai martaba Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi Ojaja II

Ooni na Ife

Osun

CFR

2

HM Omo N'Oba N'Edo Uku Akpolokpolo Ewuare

Oba na Benin

Edo

CFR

3

Mai martaba, Alhaji Aminu Ado Bayero

Sarkin Kano

Kano

CFR

4

Mai martaba Ahmed Nuhu Bamali

Sarkin Zazzau

Kaduna

CFR

5

Mai martaba Prof James Ortese Ayatse

Tor Tiv V

Benue

CFR

6

Mai martaba Abubakar Shehu Abubakar III

Sarkin Gombe

Gombe

CFR

7

Mai martaba Alh. Muhammadu ibn Abali Muhammad Idrissa

Sarkin Fika

Yobe

CFR

8

Da. Jacob Gyang Buba

Gbong Gwom Jos

Plateau

CFR

9

Mai martaba Justice Sidi Bage Muhammad I (JSC Rtd)

Sarkin Lafia

Nasarawa

CFR

10

Mai martaba King Dandeson Douglas JAJA

King Jaja na Opobo

Rivers

CFR

11

Mai martaba Oba Gabriel Adejuwon

Onisan na Isan

Ekiti

CFR

12

Mai martaba Oba (Dr) Aladetoyinbo Ogunlade Aladelusi, Odundun II

Deji na Akure

Ondo

CFR

13

Mai martaba Oba Babatunde Adewale Ajayi

Akarigbo na Remo

Ogun

CFR

14

Mai girma Ntenyin (Dr) Solomon Daniel Etuk, JP

Oku Ibom Ibibio

Akwa Ibom

CFR

Kara karanta wannan

Shugaba Buhari Ya Karrama Buratai Da Babban Lambar Yabo Na Kasa

15

Mai martaba Igwe Amb. Lawrence Agubuzu

Igwe na Eziama

Enugu

CFR

16

Mai martaba King Alfred Diete-Spiff

Shugaban majalisar sarakunan Bayelsa

Bayelsa

CFR

17

Mai martaba Ogiame Atuwatse III

Olu na Warri

Delta

CFR

18

Mai martaba Eze (Dr) E. C. Okeke

Shugaban majalisar sarakunan Imo

Imo

CFR

19

Mai martaba Eze Joseph Ndubuisi Nwabeke

Shugaban majalisar sarakunan Abia

Abia

CFR

20

Mai martaba HRM Eze Charles N. Nkpuma

Ciyaman, Ebonyi

Ebonyi

CFR

Shugaba Buhari Ya Karrama Buratai Da Babban Lambar Yabo Na Kasa

A gefe guda, mun ji cewa tsohon babban hafsan sojojin kasan Najeriya kuma jakadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, T.Y. Buratai ya shiga jerin wadanda za su samu lambar yabo ta kasa na 'Commander of the Order of the Federal Republic', (CFR).

Tsohon shugaban sojojin da wasu fitattun yan Najeriya guda 436 ne za a karrama da lambar yabon a wannan shekarar.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Ku Sake Bawa APC Wata Damar, In Ji Dr Kailani Muhammad

Kamar yadda Legit.ng ta gano, Shugaba Muhammadu Buhari, a ranar Talata 11 ga watan Oktoba zai gabatar da lambar yabon da wadanda aka zaba a gidan gwamnati, Abuja.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng