Annoba ta Barke a Sansanin Tsoffin 'Yan Boko Haram, Wasu Sun Fara Shekawa Lahira

Annoba ta Barke a Sansanin Tsoffin 'Yan Boko Haram, Wasu Sun Fara Shekawa Lahira

  • Gwamnatin jihar Borno ta sanar da mutuwar mutum biyu daga cikin tubabbun 'yan Boko Haram sakamakon annobar amai da gudawa
  • Sai da mazauna sansanin sun tabbatar da cewa rayuka 20 aka rasa daga ranar Juma'a zuwa Asabar bayan annonar ta barke
  • Kwamishinan harkokin mata da cigaba, Zuwaira Gambo, tace an kwashe wadanda suka kamu da cutar kuma an killace ana musu magani

Borno - A kalla mutum biyu sun sheka lahira bayan annobar amai da gudawa ta barke a sansanin tsofaffin mayakan Boko Haram dake garin Maiduguri a jihar Borno.

Gwamnatin jihar Borno ta tabbatar da mutuwar a sansanin Kosheri dake kan titin Maiduguri zuwa Dikwa. Gwamnati tace da yawa daga cikin mazauna sansanin basu da lafiya kuma ana kula da su da magunguna.

Kara karanta wannan

Tashin hankali yayin da 'yan sanda suka fatattaki 'yan a mutun Peter Obi a wata jiha

Borno Map
Annoba ta Barke a Sansanin Tsoffin 'Yan Boko Haram, Wasu Sun Fara Shekawa Lahira. Hoto daga thecable.ng
Asali: UGC

Wata majiya daga sansanin ta sanar da Premium Times cewa, an rasa rayuka kusan 20 a wurin sakamakon annobar.

"Zan iya tabbatar muku da cewa annobar ta barke tun daga ranar Juma'a kuma mutum 14 sun rasa rayukansu."

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

- Majiyar tace kamar yadda ma'aikacin lafiya ya tabbatar mata.

Majiyar wacce ta bukaci a boye sunanta saboda tsaro, tace wasu mutum shida sun sake mutuwa a ranar Asabar.

Sai dai, a martanin ranar Lahadi, gwamnatin jihar Brono tace rayuka biyu aka rasa a sansanin.

"Rayuka biyu kadai aka rasa bayan barkewar annobar amai da gudawa a sansanin Kosheri."

- Kwamishinan harkokin mata da cigaba, Zuwaira Gambo ta sanar da Premium Times a ranar Asabar.

“Sauran wadanda aka gano suna dauke da cutar an kwashe su daga sansanin tare da kai su inda za a killace."

Kara karanta wannan

Taraba: Dubban jama'a sun yi wa Nyame maraba bayan Buhari yayi masa rangwame

Har a halin yanzu dai ba a fitar da sunayen wadanda suka rasa rayukansu ba a sansanin.

Duk da ba a samu jami'ai daga ma'aikatar lafiya ba domin tsokaci kan lamarin, kwamishinan harkokin matan tace:

"Duk wanda lamarin ya shafa a ma'aikatar lafiya ya je ya duba halin da sansanin yake ciki."

Sojojin Sama Sun Yi Luguden Wuta A Sansanin Gogarman Yan Bindiga Bello Turji

A wani labari na daban, 'yan bindiga masu tarin yawa na sansanin fitaccen ‘dan ta’adda Bello Turji, sun sheka lahira, jaridar PR Nigeria ta rahoto.

An halaka ‘yan ta’addan ne a wani samamen ba-zata da dakarun sojin rundunar Operation Forest Sanity suka kai dazukan Zamfara.

Harin ba-zatan an yi shi ne da jiragen yakin sojin sama bayan sun samu bayanan sirri.

Asali: Legit.ng

Online view pixel