'Yan Sanda Sun Kama Wani Mutum Yana Zagin Kabarin Wata a Wani Faifan Bidiyo
- Kafar TikTok na daya daga cikin kafafen da ke bari a yada nau'ikan bidiyo masu ban mamaki da sauran kafafe ba sa amincewa dasu
- An ga wani matashi dan jihar Kano yana runtumawa mahaifiyar abokinsa ashariya saboda wani sabani da ya shiga tsakaninsu
- Rundunar 'yan sanda ta bayyana yadda ta kamo matashin da tare fara yi masa tambayoyin don gano tushen matsalar
ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit
Jihar Kano - Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta cafke wani mutum mai suna Abdullahi Yar Dubu biyo bayan wani faifan bidiyon TikTok da ya nuna yana zagi da ruwan ashariya a kan kabarin mahaifiyar abokinsa.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa a ranar Lahadi ya tabbatar da cewa an kama ‘Yar Dubu tare da mika shi zuwa hedikwatar ‘yan sanda da ke Kano domin ci gaba da yi masa tambayoyi.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/d374ad535c65a2c8.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Shawari kyauta: Hanyoyi 15 da za ku bi domin kiyaye kanku daga fadawa matsala a Najeriya
![Yadda aka kame wani matashi da ya durawa kabarin mahaifiyarsa ashariya Yadda aka kame wani matashi da ya durawa kabarin mahaifiyarsa ashariya](https://cdn.legit.ng/images/1120/e0a3ae6f0fff7fa6.jpeg?v=1)
Asali: UGC
An ga ‘Yar Dubu a cikin faifan bidiyon yana tsaye a saman kabarin yana zagin mamaciyar da aka binne a wani lokaci a baya, rahoton Sahelian Times.
Kawo yanzu dai ba a bayyana abin da ya tunzura matashin na aikata abin da bai dace ba, amma mafi yawan masu sharhi a shafukan sada zumunta sun nuna fushi da kin amincewa da maganganun nasa.
DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka
An kuma ji ‘Yar Dubu a cikin faifan bidiyon yana kalubalantar abokin nasa da ya same shi a makabarta domin su fuskanci juna.
Martanin 'yan soshiyal midiya
Hausa Arewa Medium ta yada bidiyon a Facebook tare da bayyana labarin kawo 'Yar Dubu, kuma jama'a da dama sun yi martani game da maganganun matashin.
Ga dai abin da suke cewa:
@Al Mustapha Zainu ya ce:
"Masha Allah aigonda da akaka masa saboda abinda yayi yasaba ma addini mu kawai aimasa hukunci mai tsanani saboda idan wani yagani ba zaigodaba."
@Sadiq A Saidu ya ce:
"Masha Allah sunyi dai dai wlh nadade Banga tashin hankali irin wannanba Allah yasa mufi karfin zuciyarmu."
@Lawal Usman ya ce:
"Jahilci ciyo ne, Allah ka karemu daga sharrin son zuciya alfarma annabi."
@Fatima Adam ta ce:
"Kiji wata lukutar masifa mutum ya mutu ma baa kyaleshi ya kwanta lafiya ba to allah shi kyauta."
@Anas Iliyasu ya ce:
"Innalillahi wa inna ilaihirirraji, un,,wannan bashifa da hankali,,, dan daudu ne fa,,."
Garkuwa da mutane: Alkali ta yanke hukunci a kan Budurwar da tayi karyar an sace ta
A wani labarin, dazu wani karamin kotun majistare da ke zama a unguwar Wuse 2 a garin Abuja, ya saurari kara a kan wata Ameerah Sufyan mai shekara 23. Wannan Baiwar Allah ta kitsa labarin cewa an yi garkuwa da ita, alhali ba ta hannun ‘yan bindiga.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/e3f4fa2751256f00.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Komai Ya Ji: Bidiyoyin Wata Zukekiyar Amarya Da Angonta Sun Haddasa Cece-kuce, Sun Hadu Matuka
A kan haka ne ‘yan sanda suka kai kararta a kotu. Rahoton da jaridar Punch ta fitar dazu, ya tabbatar da cewa Sufyan ta amsa laifin ta da bakinta.
Da ta bayyana a gaban Alkali Chukwuemeka Nweke a ranar Laraba, 29 ga watan Yuni 2022, Ameerah Sufyan ta amsa duka zargin da suke wuyanta.
Asali: Legit.ng