Da Dumi-Dumi: Masu Gidajen Burodi Za Su Tsinduma Yajin Aiki Na Kasa Baki Daya A Najeriya

Da Dumi-Dumi: Masu Gidajen Burodi Za Su Tsinduma Yajin Aiki Na Kasa Baki Daya A Najeriya

Kungiyar masu gidajen burodi ta 'Premium Breadmakers Association of Nigeria (PBAN) da ta kunshi direktoci da masu hadin gwiwa ta kammala shirin fara yajin aikin gargadi na kwana hudu daga ranar Alhamis 21 ga watan Yulin 2022.

Masu gidajen burodin sun dauki wannan matakin ne don kokawa kan hauhawar farashin kayan yin burodi a kasar suna cewa aiki na gagararsu a kasar, rahoton Daily Trust.

yanzu
Da Dumi-Dumi: Masu Gidajen Burodi Za Su Tsinduma Yajin Aiki A Najeriya
Asali: Original

Bugu da kari, sun bukaci hukumar NAFDCA ta rage kudin tara wato N154,000 da ta ke karba ga kamfanonin burodi wadanda ba su sabunta lasisinsu ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

PBAN ta kuma yi kira ga gwamnati ta bawa mambobinta bashi masu saukin ruwa da babban bankin kasa, CBN, ke bawa kanana da matsakaitan yan kasuwa (MSMEs).

Kara karanta wannan

Karin bayani: Wani shugaban APC ya yi ta maza, ya tsere daga hannun 'yan bindiga

Kungiyar ta kuma bukaci a rage yawan hukumomi da ke sa ido kan ayyukan masu gidajen burodin.

Dakaci karin bayani ...

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164