An gurfanar da wani matashi kan satar Fankar Masallaci a Bauchi, an yanke masa hukunci

An gurfanar da wani matashi kan satar Fankar Masallaci a Bauchi, an yanke masa hukunci

  • An cika hannu da wani matashi a jihar Bauchi kan laifin satar fanka a Masallaci
  • Kotun Shari'a dake jihar ta yanke masa hukuncin daurin wata goma sha biyar a gidan kurkuku
  • Jihar Bauchi na daya daga cikin jihohin Arewacin Najeriya da akwai kotunan Shari'ar Musulunci

Bauchi - An damke wani mutumi mai suna Salisu Aliyu kan zargin satar Fanka a cikin Masallacin garejin motar Dass dake karamar hukumar Dass, jihar Bauchi.

Ba tare da bata lokaci ba an gurfanar da matashin dan shekara 25 gaban kotun Shari'a ta biyu dake jihar, rahoton Leadership.

A kotu, Salisu Aliyu, ya amsa laifin cewa lallai ya aikata wannan laifi.

Alkalin kotun, Mukhta, ya jefashi kurkukun daurin watanni 15 a gidan kaso amma an bashi zabin biyan tara N30,000 da bulala 50.

Kara karanta wannan

Adamu Aliero, Dakingari Da Wasu Jiga-Jigan APC a Kebbi Sama Da 30 Sun Sauya Sheka Zuwa PDP

Sharia
An gurfanar da wani matashi kan satar Fankar Masallaci a Bauchi, an yanke masa hukunci Hoto
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng