Yanzu-Yanzu: Jami'an tsaro sun budewa magoya bayan Okorocha wuta a farfajiyar gidansa

Yanzu-Yanzu: Jami'an tsaro sun budewa magoya bayan Okorocha wuta a farfajiyar gidansa

  • Jami'an tsaro a halin yanzu sun bude wa magoya bayan Sanata Rochas Okorocha wuta a farfajiyar gidansa da ke Abuja
  • Magoya bayan da yawancinsu mata ne da manema labarai a halin yanzu sun cika bujensu da iska domin gudun ceton rayukansu
  • Jami'an tsaro sun zagaye gidan fitaccen dan siyasan in da suka jaddada cewa ba za su bar wurin ba har sai sun cafke shi

FCT, Abuja - Jami'an tsaro da ke zagaye da gidan tsohon gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha, a Abuja sun bude wa magoya bayan dan majalisar wuta domin tarwatsa su.

Masu zanga-zangar wadanda da yawansu mata ne da manema labarai da ke kula da cigaban, a halin yanzu suna gudun ceton rayukansu.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Jami'an EFCC sun tasa keyar sanata Okorocha daga gidansa

Jami'an tsaron suna jaddada cewa ba za su bar farfajiyar gidan ba har sai an damke dan siyasar, Daily Trust ta ruwaito.

Yanzu-Yanzu: Jami'an tsaro sun budewa magoya bayan Okorocha wuta a farfajiyar gidansa
Yanzu-Yanzu: Jami'an tsaro sun budewa magoya bayan Okorocha wuta a farfajiyar gidansa
Asali: Original

Karin bayani na nan tafe...

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Khalid avatar

Aisha Khalid (Hausa editor) Aisha Khalid marubuciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018. Ta kwashe shekaru tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu. Za a iya tuntubar ta a adireshin email din ta kamar haka: aisha.khaleed@corp.legit.ng