Yanzu-Yanzu: Jami'an tsaro sun budewa magoya bayan Okorocha wuta a farfajiyar gidansa

Yanzu-Yanzu: Jami'an tsaro sun budewa magoya bayan Okorocha wuta a farfajiyar gidansa

  • Jami'an tsaro a halin yanzu sun bude wa magoya bayan Sanata Rochas Okorocha wuta a farfajiyar gidansa da ke Abuja
  • Magoya bayan da yawancinsu mata ne da manema labarai a halin yanzu sun cika bujensu da iska domin gudun ceton rayukansu
  • Jami'an tsaro sun zagaye gidan fitaccen dan siyasan in da suka jaddada cewa ba za su bar wurin ba har sai sun cafke shi

FCT, Abuja - Jami'an tsaro da ke zagaye da gidan tsohon gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha, a Abuja sun bude wa magoya bayan dan majalisar wuta domin tarwatsa su.

Masu zanga-zangar wadanda da yawansu mata ne da manema labarai da ke kula da cigaban, a halin yanzu suna gudun ceton rayukansu.

Jami'an tsaron suna jaddada cewa ba za su bar farfajiyar gidan ba har sai an damke dan siyasar, Daily Trust ta ruwaito.

Yanzu-Yanzu: Jami'an tsaro sun budewa magoya bayan Okorocha wuta a farfajiyar gidansa
Yanzu-Yanzu: Jami'an tsaro sun budewa magoya bayan Okorocha wuta a farfajiyar gidansa
Asali: Original

Karin bayani na nan tafe...

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Asali: Legit.ng

Online view pixel