Rundunar Sojin Saman Najeriya, NAF, Ta Ɗage Bikinta Saboda Fashewar 'Tulun Gas' a Kano

Rundunar Sojin Saman Najeriya, NAF, Ta Ɗage Bikinta Saboda Fashewar 'Tulun Gas' a Kano

  • Rundunar Sojin Saman Najeriya, NAF, ta dage bikinta da aka shirya yi a ranar Alhamis zuwa Asabar a Kano.
  • Mai magana da yawun NAF, Edward Gabkwet, ya ce an dage bikin ne saboda afkuwar wasu abubuwa da ba a yi tsammani ba
  • Amma, wani babban jami'i na NAF, ya bayyana cewa fashewar 'tulun gas' din a Kano ne ya sa aka dage taron don kara inganta tsaro

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Mahukunta na Rundunar Sojojin Saman Najeriya, NAF, sun dage bikin da aka shirya yi a Kano na shekarar 2022.

Daily Trust ta rahoto cewa da farko an shirya yin bikin ne a ranar Alhamis amma an matsar da shi zuwa ranar Asabar.

Rundunar Sojin Saman Najeriya, NAF, Ta Ɗage Bikinta Saboda Fashewar 'Tulun Gas' a Kano
Rundunar Sojin Saman Najeriya, NAF, Ta Ɗage Bikinta Saboda Fashewar Wani Abu a Kano. Hoto: Daily Trust.
Asali: Twitter

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kara karanta wannan

Sokoto: An ayyana neman wadanda aka gani a bidiyon kone dalibar da ta zagi Annabi

Duk da cewa kakakin NAF, Edward Gabkwet, wanda ya fitar da sanarwar a Abuja bai bayyana dalilin dage bikin ba, wani babban jami'i na rundunar ya ce fashewar abu a Kano ne dalilin.

Jami'in ya ce:

"Bayan fashewar abu a Sabon Garin Kano a yanzu, unguwar da za a yi bikin mu na 2022, akwai bukatar mu sake karfafa tsaro a yankin kafin fara bikin don gudun abin da ka iya faruwa."

Daily Trust ta rahoto cewa a kalla mutane uku ne suka mutu sakamakon fashewar abin kuma a yanzu wasu gini ya danne su.

Amma, yayin fitar da sanarwar, Gabkwet, mai mukamin Air Commodore, ya ce an dage bikin ne 'saboda wasu abubuwa da ba a yi tsammanin faruwarsu ba."

Ya ce:

"Bikin Ranar Rundunar Sojin Saman Najeriya, NAF, na 2022 da aka shirya yi daga ranar 19 - 21 ga watan Mayu a NAF Base, Kano yanzu an dage shi zuwa ranar 21 - 23 na Mayun 2022 a wurin da aka shirya yi tunda farko.

Kara karanta wannan

Yadda Jam’iyyar APC ta samu tayi wa Yari, Marafa da Gwamna Matawalle sulhu a Zamfara

"An yi canjin ne saboda faruwar wasu abubuwa da ba a yi tsammani ba. NAF tana bawa dukkan bakin da aka gayyata hakuri don abin da canjin zai haifar musu."

Saurari karin bayani ...

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164