2023: Kotu ta aika dan takarar gwamna na PDP gidan gyara hali

2023: Kotu ta aika dan takarar gwamna na PDP gidan gyara hali

Rivers - Babbar kotun jihar Ribas, a ranar Litinin, 16 ga watan Mayu, ta saka ranar sauraron bukatar bayar da belin dan takarar gwamna na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a jihar Ribas, Hon. Farah Dagogo, wanda ke tsare.

Jaridar Leadership ta rahoto cewa alkalin kotun, Mai shari’a Chinwendu Nworgu, ya tsayar da ranar Juma’a, 20 ga watan Mayu domin zama kan lamarin.

Don haka, Nworgu, ya yi umurnin mayar da Dagogo wanda ya kuma kasance dan majalisar wakilai gidan gyara hali da ke Port Harcourt.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng