Ganduje ya ɗauki mataki bayan shugaban ma'aikatan fadar gwamnati ya koma NNPP

Ganduje ya ɗauki mataki bayan shugaban ma'aikatan fadar gwamnati ya koma NNPP

  • Bayan sauya shekar shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin Kano zuwa NNPP, Ganduje ya ba da umarnin a kula harkokin ofishin
  • Gwamnan ya ba shugaban ma'aikatan Kano, Usman Bala, ya kula da ofishin kafin ya maye gurbinsa saboda ya na da kwarewa a fannin
  • Tsohon shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin, Makoda, ya aje aikinsa tare da sauya sheka daga APC zuwa NNPP da ake ya yi

Kano - Gwamnan Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya umarci shugaban ma'aikata, Usman Bala, ya rike ofishin tsohon shugaban ma'aikatan fadar gwamnati, Ali Haruna Makoda.

Daily Trust ta rahoto cewa gwamnan ya ɗauki wannan matakin ne biyo bayan sauya shekar Makoda daga APC zuwa jam'iyyar NNPP mai kayan marmari.

Gwamna Ganduje ya maye gurbin Makoda na wucin gadi.
Ganduje ya ɗauki mataki bayan shugaban ma'aikatan fadar gwamnati ya koma NNPP Hoto: thisdaylive.com
Asali: UGC

Legit.ng Hausa ta kawo muku rahoton yadda shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin ya aje aikinsa, kana ya fice daga APC ya koma jam'iyyar da ake ya yi wato NNPP.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Ministan Buhari ya fadi ranar da zai yi murabus, zai dukufa ga takara

Mista Makoda, wanda tun farko gwamna Ganduje ya ki amincewa da murabus dinsa, ya na da burin neman kujerar ɗan majalisar wakilai a 2023, inji wata majiya.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A wata sanarwa, kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Muhammad Garba, ya ce Gwamna Ganduje ya umarci Usman ya kula da harkokin ofishin shugaban ma'aikatan gidan gwamnati.

Kwamishinan ya ce gwamna Ganduje ya ɗauki wannan matakin ne kafin zaƙulo wanda zai maye gurbin Makoda, wanda ya fice daga APC.

A wani sashin sanarwan, Muhammad Garba ya ce:

"Gwamna Ganduje ya nuna kwarin guiwarsa da fatan cewa za'a samu kyakkyawar kula da tafiyar da harkokin ofishin daga hannun Usman, kasancewar ya taɓa rike muƙamin."

Makoda ya yi aiki a matsayin kwamishinan Muhalli a zangon mulkin Ganduje na farko, daga bsani ya koma ofishin shugaban ma'aikatan gwamnan jihar Kano.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Bidiyon Kwankwaso Ya Isa Gidan Shekarau Don 'Ƙarasa' Maganan Komawarsa NNPP

Batun sauya shekara Shekarau ya yi zafi a Kano

A wani labarin kuma Dirama a Kano yayin da tawagar Kwankwaso ta dira gidan Shekarau awanni bayan tafiyar Ganduje

Siyasar Kano ta ƙara rikicewa musamman tsakanin gwamna Abdullahi Umar Ganduje da Sanata Ibrahim Shekarau.

Bayan ziyarar Ganduje gidan Shekarau don hana shi komawa NNPP, Kwankwaso ya tura tawaga kafin zuwansa gidan Shekarau.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262