Hukumar yan sanda ta damke dillalan makamai da bindigogin AK47 guda 57 a Jos

Hukumar yan sanda ta damke dillalan makamai da bindigogin AK47 guda 57 a Jos

  • Jami'an yan sanda sun samu gagarumar nasarar damke masu safarar makamai a garin Jos, birnin jihar Flato
  • Daga cikin abubuwan da aka gano hannunsu akwai bindigogin Ak-47 guda hamsin da bakwai
  • Kakakin hukumar yace an kaddamar da bincike don bibiyan abokar harkarsu da wadanda suke sayarwa makamai

Birnin tarayya Abuja - Hukumar yan sandan Najeriya ta damke masu safarar makamai hudu a Jos, jihar Plateau dauke da bindigogin AK47 guda hamsin da bakwai (57).

Kaakin hukumar, CSP Muyiwa Adejumobi, a jawabin da ya fitar ranar Alhamis yace matasa hudu masu matsakaicin shekaru kuma duka mazauna Jos na wannan harkar.

A cewarsa, an damke su ne sakamakon harin sirri da aka musu.

Yace:

"Jami'in rundunar FIB-IRT a harn sirri, sun damke wasu dilolin makamai hudu kuma sun kwato bindigar AK47 guda 57 da dinbin harsasai a Jos da wasu jihohi."

Kara karanta wannan

2023: PDP ta soke 6 daga cikin yan takararta na sanata a jihar Kogi

"Matasan sune Hamza Zakari (aka Hamzo) dan shekara 20, Abubakar Muhammed (aka Fancy) dan shekara 22, Umar Ibrahim dan shekara 25 da Muhammed Abdulkarim (aka Dan-Asabe) dan shekara 37, duka mazauna Jos."

Dillalan makamai da bindigogin AK47 guda 57 a Jos
Hukumar yan sanda ta damke dillalai makamai da bindigogin AK47 guda 57 a Jos Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

Ya kara da cewa sun amsa laifin da ake zarginsu da shi kuma an gano suke dillancin makamai wa yan bindiga dake addaban al'ummar yankin.

A cewarsa, an kaddamar da bincike don bibiyan abokan harkarsu da wadanda suke sayarwa makamai.

Nasara daga Allah: Sojoji sun kashe kwamandan ISWAP, sun ceto mutane 848 da aka sace

Hedikwatar tsaron Najeriya a ranar Alhamis ta sanar da cewa, a kalla mutane 848 da aka yi garkuwa da su ne sojoji suka kubutar a wani samame daban-daban a fadin kasar cikin makwanni uku da suka gabata.

Kara karanta wannan

Kar kuce zaku rama: Kwamandan Civil Defence ya yi gargadi kan harin da MOPOL suka kai musu

Jaridar Punch ta rahoto cewa, da yake jawabi yayin wani taron manema labarai a Abuja, Daraktan ayyukan yada labarai na tsaro, Janar Benard Onyeuko, ya kuma ce sojoji sun kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar ISWAP, Abubakar Dan-Buduma.

Ya kara da cewa an kuma kama masu kwarmato bayanai na ‘yan ta’addan a ayyuka daban-daban tsakanin 7 da 28 ga Afrilu, 2022.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng