Hukumar yan sanda ta damke dillalan makamai da bindigogin AK47 guda 57 a Jos
- Jami'an yan sanda sun samu gagarumar nasarar damke masu safarar makamai a garin Jos, birnin jihar Flato
- Daga cikin abubuwan da aka gano hannunsu akwai bindigogin Ak-47 guda hamsin da bakwai
- Kakakin hukumar yace an kaddamar da bincike don bibiyan abokar harkarsu da wadanda suke sayarwa makamai
Birnin tarayya Abuja - Hukumar yan sandan Najeriya ta damke masu safarar makamai hudu a Jos, jihar Plateau dauke da bindigogin AK47 guda hamsin da bakwai (57).
Kaakin hukumar, CSP Muyiwa Adejumobi, a jawabin da ya fitar ranar Alhamis yace matasa hudu masu matsakaicin shekaru kuma duka mazauna Jos na wannan harkar.
A cewarsa, an damke su ne sakamakon harin sirri da aka musu.
Yace:
"Jami'in rundunar FIB-IRT a harn sirri, sun damke wasu dilolin makamai hudu kuma sun kwato bindigar AK47 guda 57 da dinbin harsasai a Jos da wasu jihohi."
"Matasan sune Hamza Zakari (aka Hamzo) dan shekara 20, Abubakar Muhammed (aka Fancy) dan shekara 22, Umar Ibrahim dan shekara 25 da Muhammed Abdulkarim (aka Dan-Asabe) dan shekara 37, duka mazauna Jos."

Asali: Twitter
Ya kara da cewa sun amsa laifin da ake zarginsu da shi kuma an gano suke dillancin makamai wa yan bindiga dake addaban al'ummar yankin.
A cewarsa, an kaddamar da bincike don bibiyan abokan harkarsu da wadanda suke sayarwa makamai.
Nasara daga Allah: Sojoji sun kashe kwamandan ISWAP, sun ceto mutane 848 da aka sace
Hedikwatar tsaron Najeriya a ranar Alhamis ta sanar da cewa, a kalla mutane 848 da aka yi garkuwa da su ne sojoji suka kubutar a wani samame daban-daban a fadin kasar cikin makwanni uku da suka gabata.

Kara karanta wannan
Kar kuce zaku rama: Kwamandan Civil Defence ya yi gargadi kan harin da MOPOL suka kai musu
Jaridar Punch ta rahoto cewa, da yake jawabi yayin wani taron manema labarai a Abuja, Daraktan ayyukan yada labarai na tsaro, Janar Benard Onyeuko, ya kuma ce sojoji sun kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar ISWAP, Abubakar Dan-Buduma.
Ya kara da cewa an kuma kama masu kwarmato bayanai na ‘yan ta’addan a ayyuka daban-daban tsakanin 7 da 28 ga Afrilu, 2022.
Asali: Legit.ng