Rudani da tashin hankali: An tsinci gawawwaki da harsasai jikinsu a wata gonar Abuja
- Mazauna anguwar Kamadi cikin yankin Kwali dake birnin tarayya sun shiga firgici bayan an tsinci gawawwaki masu dauke da harsasai a wata gona
- Mutanen anguwan sun zargi gawawwakin da zama na masu garkuwa da mutane ko kuma wadanda aka yi garkuwa dasu
- Wani jami'in 'dan sandan yankin ya tabbatar wa manema labarai yadda aka kai daya daga cikin gawawwakin UATH na Gwagwalada, yayin da dayar gawar ta riga ta rube
Abuja - Mazauna anguwan Kamadi a yankin Kwali dake birnin tarayya (FCT) sun shiga rudani bayan an tsinci wasu gawawwaki guda biyu masu dauke da harsasai a wata gonar yankin.
Wani mazaunin yankin, Joshua Dogo, ya bayyana yadda a ranar Laraba wasu 'yan kauye, yayin dawowa daga gonarsu misalin karfe 5:00 na yamma suka ga gawawwakin guda biyu cikin wata gonar ayaba.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/4195a967ae759c23.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
An Shawarci Al'umma Su Ƙauracewa Naman Shanu Na Sati Ɗaya Bayan Shanu 20 Sun Yi Mutuwar Ban Mamaki a Kogi
![Rudani da tashin hankali: An tsinci gawawwaki da harsasai jikinsu a wata gonar Abuja Rudani da tashin hankali: An tsinci gawawwaki da harsasai jikinsu a wata gonar Abuja](https://cdn.legit.ng/images/1120/542d4565184ded60.jpeg?v=1)
Asali: UGC
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Ya cigaba da bada labarin yadda suke zargin gawawwakin masu garkuwa da mutane ne ko kuma wadanda aka yi garkuwa dasu.
Wani jami'in 'dan sanda a marabar Kwali, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya tabbatar wa Daily Trust game da abunda aka gani, inda ya ce an aje daya daga cikin gawawwakin a asibitin koyarwa na Abuja (UATH) a gwagwalada.
Ya kara da cewa, "Dayar gawar ta riga ta rube. Muna jiran shugaban yankin ya amince wa sashin kula da muhalli damar birne gawar a wurin."
Daily Trust ta ruwaito cewa, yayin martani, shugaban yankin, Danladi Chiya, ya ce za a amince da hakan kafin lokacin tashin aiki ya yi.
Kaduna: 'Yan bindiga sun kai mugun farmaki sansanin soji, sun sheke dakaru 11
A wani labari na daban, a kalla sojoji 11 ne aka kashe a mugun hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a wani sansanin soji da ke karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, kamar yadda majiya ta shaida wa TheCable.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/82c471f67c9d4045.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Wajibi ne APC ta lashe zabe a 2023 saboda ban taba rashin nasara ba, Abdullahi Adamu
‘Yan bindigar da suka isa sansanin da yawansu sun kutsa cikin sansanin da ke kauyen Polwire a ranar Litinin da ta gabata inda suka yi artabu da sojojin.
Majiyar soji ta shaida wa jaridar TheCable cewa, ‘yan bindigar sun bayyana a kan babura kuma suna dauke da manyan makamai da suka hada da gurneti (RPG).
Asali: Legit.ng