Yanzu-yanzu: An nada Sheikh Nuru Khalid limanci a sabon Masallaci a Abuja

Yanzu-yanzu: An nada Sheikh Nuru Khalid limanci a sabon Masallaci a Abuja

Abuja - Limamin Masallacin da aka kora a rukunin gidajen yan majalisu dake birnin tarayya Abuja, Sheikh Nuru Khalid, ya samu sabon limanci a masallacin Juma'a.

Kwamitin wata Masallacin Juma'a dake bayan rukunin gidajen babban bankin tarayya CBN dake Abuja ta nada shi, rahoton TheNation.

Ranar Juma'a, 18 ga Afrilu zai fara jagorantar jama'a a Masallacin.

Sheikh Nuru Khalid
Yanzu-yanzu: An nada Sheikh Nuru Khalid limanci a sabon Masallaci a Abuja Hoto: Al Afriky
Asali: Twitter

Sheikh Khalid yace:

"Da yardar Allah zan fara jagoranci a sabon Masallacin ranar Juma'a, saboda a matsayinmu na Malamai muna bukatan wajen ibada."
"Akwai Masallacin Juma'an da muka gina bayan CBN Quaters a Abuja; can zan fara limancin yanzu."

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng