Duk za mu mutu: Yaro ya fashe da kuka, yana tsoron ka da Rasha ta harbo bam Najeriya

Duk za mu mutu: Yaro ya fashe da kuka, yana tsoron ka da Rasha ta harbo bam Najeriya

  • Wani karamin yaro dan Najeriya ya bar mutane cikin mamaki da dariya bayan da aka gan shi yana sharbar kuka saboda mamayar da Rasha ke ci gaba da yi a Ukraine
  • A lokacin da wata mata ta tambaye shi, yaron ya bayyana fargabar cewa Rasha za ta aika bama-bamai domin hallaka kowa a fadin Najeriya
  • Amsar da ya bayar ta ba matar da mamaki amma yaron ya tsaya tsayin daka cewa ba ya son ya mutu a irin wannan yanayi na yaki

Najeriya - Yayin da mamayar da Rasha ta yi wa Ukraine ke ci gaba da samun tofin Allah tsine a duniya daga shugabannin duniya, wani karamin yaro ya shiga cikin rudani yayin da ya bayyana fargabar abin da yake tunani.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Wani mutum ya daba wa mahaifiyarsa wuka har lahira yayin da yake fada da matarsa a Neja

A ranar 24 ga watan Fabrairu, shugaban kasar Rasha ya ba da sanarwar kaddamar da farmakin soji a yankin Donbas na gabashin Ukraine, matakin da ya sa aka kakaba wa Rasha takunkumi daga kasashe daban-daban.

Kowa zai mutu: Yaro ya fashe da kuka saboda tsoron bam daga Putin
Duk za mu mutu: Yaro ya fashe da kuka, yana tsoron ka da Rasha ta harbo bam Najeriya | Hoto: @saintavenue_ent1 a shafin Instagram, Pavel Bednyakov a Getty Imgaes
Source: Getty Images

A wani sabon faifan bidiyo da @saintavenue_ent1 ya yada a Instagram, wata mata ta tambayi wani karamin yaro yayin da yake sharbar kuka.

Yaron ya ce yana sharbar kuka ne saboda tsoron rasa ransa domin kuwa Rasha ta aika bama-bamai domin lalata Najeriya, a fahimtarsa.

Cikin kuka ya ce idan Rasha ta yi haka babu wanda zai tsira a Najeriya har da shi kansa yaron.

A cewarsa:

“Idan (Rasha) suka aika bam zuwa Najeriya, yanzu dukkanmu za mu mutu.”

Da alamu dai bai fahimci ya lamarin yake ba, wannan yasa matar ta kyalkyale da dariya.

Kalli bidiyon:

Martanin 'yan soshiyal midiya

'Yan Najeriya sun mayar da martani game da bidiyon yaron, ga kadan daga ciki:

@e_smiler_ ya ce:

"Mutumin da bai taba sanin komai ba a rayuwa, da gaskiyarka bro."

Kara karanta wannan

Babu dadi: IGP ya koka kan yadda 'yan sanda ke amfani da makamai ta wasu hanyoyi

@bdrickcool ne ya rubuta

"Ba ka so ka shiga aljanna ne kuma?"

@eniadefunkebu1 yayi sharhi da cewa:

"Haka ne, nima naji tsoro oo amma irin wannan ba zai faru ba a Nigeria da sunan Yesu, Amin."

Mun zo taya ku yakar Rasha: Dandazon 'yan Najeriya sun cika ofishin jakadancin Ukraine

A wani labarin, kimanin matasa 115 ‘yan Najeriya ne, a ranar Talata, 1 ga watan Maris, suka nuna sha'awar shiga yakin kasar Ukraine da Rasha.

Matasan da suka yiwa ofishin jakadancin Ukraine da ke Abuja babban birnin Najeriya kawanya, sun kuma sanya sunayensu a cikin wata rajista da ofishin jakadancin ya bayar.

Jaridar Guardian ta rawaito cewa jami'an ofishin jakadancin sun dakile yunkurin daukar hotunan mutane a bakin ofishin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng