Allah ya yiwa mahaifin tsohon kwamishinan yan sandan Kano ‘Singam’ rasuwa

Allah ya yiwa mahaifin tsohon kwamishinan yan sandan Kano ‘Singam’ rasuwa

  • Mahaifin tsohon kwamishinan yan sandan jihar Kano, CP Muhammad Wakili, Alhaji Buba Turaki, ya rigamu gidan gaskiya
  • Marigayin wanda ya kasance tsohon jami’in hukumar Kwastam na Najeriyan ya rasu a safiyar yau Lahadi, 6 ga watan Fabrairu
  • Za a yi jana’izarsa da misalin karfe 2:00 na rana a kofar Fadar mai martaba Sarkin Gombe

Allah ya yiwa wani tsohon jami’in hukumar Kwastam na Najeriya, Alhaji Buba Turaki, rasuwa.

Marigayin wanda ya kasance mahaifi ga tsohon kwamishinan yan sandan jihar Kano, CP Muhammad Wakili wanda aka fi sani da Singam ya rasu a safiyar yau Lahadi, 6 ga watan Fabrairu, a jihar Gombe.

Allah ya yiwa mahaifin tsohon kwamishinan yan sandan Kano ‘Singam’ rasuwa
Allah ya yiwa mahaifin tsohon kwamishinan yan sandan Kano ‘Singam’ rasuwa Hoto: Aminiya
Source: UGC

Ya rasu yana da shekaru 106 a duniya bayan ya yi fama da rashin lafiya, jaridar Aminiya ta rahoto.

Alhaji Turaki ya rasu ya bar matan aure da ’ya’ya 10, maza biyar da mata biyar.

Kara karanta wannan

Hadarin mota: Kwanaki bayan kammala digiri a ABU, matashi da mahaifiyarsa sun rasu a hadari

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Aminiya ta kuma rahoto cewa za a gudanar da jana’izarsa da misalin karfe 2:00 na rana a kofar Fadar mai martaba Sarkin Gombe.

Hadarin mota: Kwanaki bayan kammala digiri a ABU, matashi da mahaifiyarsa sun rasu a hadari

A wani labarin kuma, mun ji cewa Allah ya yiwa wani dalibin jami'ar Ahmadu Bella University (ABU), Zaria, wanda ya kammala karatu kwanan nan, Bashir Maiwada Zubairu, rasuwa.

A wani wallafa da shafin Instablog9ja ya yi a Instagram, an tattaro cewa Maiwada ya rasu ne tare da mahaifiyarsa a wani hatsarin mota.

Mummunan al'amarin ya afku ne a ranar Asabar, 5 ga watan Fabrairu, a hanyar Kano zuwa Katsina.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng