Na kashe mutane sama da 20 amma yanzu na tuba, Yaron Turji da aka damke

Na kashe mutane sama da 20 amma yanzu na tuba, Yaron Turji da aka damke

  • Jami'an yan sandan Najeriya sun cika hannu da daya daga cikin dan ta'adda Bello Turji a jihar Katsina
  • Matashin dan shekara 21 ya bayyana adadin mutanen da ya kashe a baya amma yanzu ya koma ga Allah
  • Hukumar yan sandan ta bayyana cewa tana cigaba da bincike kuma zata gurfanar da shi

Funtua - Naziru Sani, daya daga cikin yaron dan bindiga Bello Turji, ya bayyana adadin mutanen da ya kashe a hare-haren da suka kai amma yanzu ya tuba bayan shiga hannu.

Dan ta'addan ya bayyana hakan yayin hira da manema da Kakakin yan sandan jihar, SP Gambo Isah, ya shirya a hedkwatar hukumar ranar Talata, rahoton Vanguard.

Naziru, wanda dan asalin garin Tsafe ne a jihar Zamfara ya shiga hannu ne a karamar hukumar Funtua, jihar Katsina, SP Gambo ya bayyana.

Kara karanta wannan

Nasara: 'Yan sanda sun halaka 'yan ta'adda 23, sun yi ram da 'yan bindiga 37 a Sokoto

Naziru yace:

"Da ni aka kai hare-hare karkashin umurnin maigidana Turji, kuma na kashe mutum 20 a baya amma na tuba yanzu."
"Na gudu daga dajin Jangebe a Zamfara inda Turji yake kai hare-hare yanzu. Na gamu da yan sanda a Funtua, yayinda nike kokarin zuwa Suleja a jihar Neja inda iyaye na suke.Na bar matata da yarana a garin Makera, Tsafe jihar Zamfara."

Yaron Turji da aka damke
Na kashe mutane sama da 20 amma yanzu na tuba, Yaron Turji da aka damke Hoto: Vanguard
Asali: Facebook

Kudin da Turji ke biyan yaransa

Yayinda aka tambayesa adadin yaran da Bello Turji ke da su kuma nawa yake biyan yaransa, Naziru yace:

"Muna da yawa. Ban san takamammen adadin ba amma akwai daruruwa kuma ina samun tsakanin N20,000 da N30,000 bayan kowani hari."

Kakakin yan sanda, SP Gambo Isah, ya bayyanawa yan jarida cewa:

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Likitan Bello Turji da ke masa jinya da kawo masa kwaya ya shiga hannu

"Bisa da labaran leken asiri, hukumar ta samu nasarar damke Naziru Sani dan garin Makera, karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara, wani dan ta'adda da ya addabi Katsina da kewaye."

Likitan Bello Turji da ke masa jinya da kawo masa kwaya ya shiga hannu

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa, an kama wani likita da ake zargin ya yi jinyar harbin bindiga ga dan ta'adda Bello Turji a jihar Sokoto.

An kama likitan mai suna Abubakar Kamarawa ne a wani gagarumin samame da jami’an tsaro suka kai kan 'yan ta'addan.

An kama shi ne tare da wasu 'yan ta'addan a wasu ayyuka daban-daban a fadin kananan hukumomi uku na jihar Sokoto.

Kananan hukumomin sun hada da, Illela, Rabah da Goronyo, duk a yankin gabashin Sokoto.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng