Ci gaba: Gwamnatin Buhari za ta gina layin dogo daga Minna zuwa tashar jiragen ruwa ta Baro a Neja

Ci gaba: Gwamnatin Buhari za ta gina layin dogo daga Minna zuwa tashar jiragen ruwa ta Baro a Neja

  • Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari za ta sake gina karamin layin dogo daga garin Minna, babbar birnin jihar Neja zuwa tashar jiragen ruwa ta Baro
  • FG ta ce ta dauki wannan mataki ne domin bunkasa harkokin tattalin arziki a jihar ta Neja da jihohin da ke makwabtaka
  • Tuni ta amince da bayar da kwangilar sake gina shi a zaman majalisar zartarwa da aka yi a yau Laraba, 19 ga watan Janairu

Neja - Gwamnatin tarayya ta sanar da shirinta na sake gina wani karamin layin dogo daga garin Minna, babbar birnin jihar Neja zuwa tashar jiragen ruwa ta Baro.

Gwamnatin ta ce ta dauki wannan mataki ne domin bunkasa harkokin tattalin arziki a jihar ta Neja da jihohin da ke makwabtaka.

Ci gaba: Gwamnatin Buhari za ta gina layin dogo daga Minna zuwa tashar jiragen ruwa ta Baro a Neja
Ci gaba: Gwamnatin Buhari za ta gina layin dogo daga Minna zuwa tashar jiragen ruwa ta Baro a Neja Hoto: Femi Adesina
Asali: Facebook

Mai ba shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara kan kafofin sadarwar zamani, Bashir Ahmed ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na Twitter a ranar Laraba, 19 ga watan Janairu.

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Daga dawowa hutu, yan majalisar dattawa sun shiga ganawar sirri

Ya kuma bayyana cewar an amince da bayar da kwangilar aikin sake ginin, a zaman majalisar zartarwa a yau Laraba.

Ahmed ya wallafa a shafin nasa:

"Gwamnatin tarayya za ta sake gina wani dan karamin layin dogo daga Minna zuwa tashar jiragen ruwa ta Baro a jihar Neja domin bunkasa harkokin tattalin arziki a Neja da jihohin makwabta, majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da bayar da kwangilar sake gina shi a yau."

Buhari ga 'yan Najeriya: Ku kara hakuri, saura kiris abinci ya yi araha a Najeriya

A wani labarin, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci yan Najeriya da su kara hakuri kan halin da ake ciki a yanzu na tsadar kayan masarufi.

Buhari ya bayyana cewa yawan abincin da ake nomawa a kasar, musamman fadada noman shinkafa da aka yi, zai karyar da farashin kayan abinci, ta yadda kowa zai iya siyansa.

Kara karanta wannan

Najeriya za ta yi nasara a yaki da rashin tsaro - Tinubu

Shugaban kasar ya yi magana ne a bikin kaddamar da shirin dalar shinkafa na Babban Bankin Najeriya (CBN) da Kungiyar Monoman Shinkafa ta Najeriya (RIFAN) a babban dakin baje kolin kasuwancin kasa da kasa na Abuja, rahoton Leadership.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng