Innalillahi: Diyar sarki ta rasu kwanaki kadan bayan rasuwar mahaifinta

Innalillahi: Diyar sarki ta rasu kwanaki kadan bayan rasuwar mahaifinta

  • Rahoton da ke iso mu ya bayyana cewa, diyar sarkin Ogbomoso, Farfesa Taibat Danmole ta riga mu gidan gaskiya
  • Kwanaki 28 da suka gabata ne mahaifinta, Oba Oladunni Oyewumi ya yi sallama da duniya bayan gajeriyar rashin lafiya
  • Majiya ta bayyana lokacin da za a yi jana'izar wannan baiwar Allah kamar yadda addini ya koyar

Jihar Kwara - Mutuwa ta sake sallama a gidan marigayi Soun na Ogbomoso, Oba Oladunni Oyewumi a jihar Kwara.

Oba Oyewumi ya rasu ne a ranar 12 ga watan Disamba yana da shekaru 95, inda aka tattaro cewa diyar marigayi sarkin, Farfesa Taibat Danmole ta rasu a ranar Asabar 8 ga watan Janairu tana da shekaru 71 a duniya.

Wasu majiyoyi a fadar sun shaida wa jaridar Punch a ranar Lahadi cewa Danmole ta dade tana jinya kafin ta rasu ranar Asabar, kwanaki 28 bayan da mahaifinta ya yi sallama da duniya.

Kara karanta wannan

Innalillahi: Mummunar gobara ta yi kaca-kaca da wani gida, uwa da jaririnta sun kone a Kano

Mutuwa a gidan sarautar Ogbomosho
Da dumi-dumi: Diyar sarki ta rasu kwanaki kadan bayan rasuwar mahaifinta | Hoto: naijanews.com
Asali: Facebook

Daya daga cikin majiyoyi ya ce:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“'Yar fari ga Baba ta rasu. Ta jima tana jinya kuma jiya ne hakan ya faru. Muna addu’ar Allah ya ja kwanakin wadanda suka rage mana.”

Danmole, wanda aka haifa a ranar 19 ga Maris, 1951, an tattaro cewa, za a yi jana’izarsa a ranar Lahadi da rana a Ilorin, babban birnin jihar Kwara.

Marigayiyar, wacce aka ce Farfesa ce a fannin ilimi, ta auri wani malamin jami’a, Farfesa Hakeem Danmole, wanda shi ne shugaban kwalejin nazarin al’umma da kimiyar zamantakewa a jami’ar Al-Hikmah da ke Ilorin.

Ta kasance kwamishiniyar ilimi a jihar Oyo daga 1997-1998. Ta kasance memba, Panel Visitation to The Polytechnic na Ibadan a 2011.

Rasuwar mahaifinta

A bangare guda, basaraken garjiya mai sarautar Soun na Ogbomoso, Oba Oladunni Oyewumi, Ajagungbade III, ya rasu.

Kara karanta wannan

Babban taro: Gwamnonin APC za su gana da Shugaba Buhari don tsayar da rana

Majiyoyi na kusa da sarkin a fadar sun shaida wa wakilin jaridar Punch cewa, basaraken mai shekaru 95 ya rasu ne da safiyar yau Lahadi.

Wasu majiyoyi guda biyu ne suka tabbatar da hakan a garin, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

A cewar majiyar:

“Gaskiya ne Baba ya rasu. Hakan ya faru da safiyar yau amma ba a sanar da hakan a hukumance ba.
“Ya yi rayuwa mai kyau kuma ya bar suna mai kyau da yawa. Nan ba da jimawa ba fadar za ta sanar da hakan.”

A wani labarin daban, Allah ya yi wa Olubadan na kasar Ibadan, Oba Saliu Adetunji rasuwa.

Marigayin ya rasu yana da shekaru 93 a duniya. Jaridar Punch ta tattaro cewa sarkin ya rasu ne a asibitin kwalejin jami’a dake Ibadan a jihar Oyo.

Majiyoyin fadar sun tabbatar da mutuwarsa, amma sun nemi a sakaya sunayensu.

Kara karanta wannan

Shugabancin APC: Ku hakura ku bar mun - Mustapha ya roki Almakura, Yari, Sheriff da sauransu

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.

Tags: