Yanzu-Yanzu: Gwamnati ta buɗe hanyoyin sadarwa da aka datse a jihar Katsina

Yanzu-Yanzu: Gwamnati ta buɗe hanyoyin sadarwa da aka datse a jihar Katsina

  • Bayan kwashe wata uku da rufe layukan sadarwa a jihar Katsina, gwamnati ta bada umarnin dawo da shi yau Alhamis
  • A sanarwan da hadimin gwamna Masari kan harkokin tsaro ya fitar, yace an ɗauki wannan matakin ne saboda samun saukin ayyukan yan bindiga
  • Yace dama an ɗauke sabis na wani ɗan lokaci ne a kokarin gwamnatin Masari na dakile yan bindiga da masu taimaka musu

Katsina - Gwamnatin jihar Katsina karkashin jagorancin gwamna Aminu Bello Masari, ta sanar da dawo da amfani da layukan sadarwa a sassan jihar.

Rahoton Aminiya Hausa ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta dawo da sabis da ta datse a baya a yunkurin dakile yawaitar ayyukan yan bindiga a wasu yankunan jihar.

Gwamnati ta ɗauki matakin datse hanyoyin sadarwa da wasu matakai ne a wasu kananan hukumomin jihar domin yaki da ta'addancin yan bindigan daji.

Kara karanta wannan

Karin Bayani: Gwamna Masari ya dira gidan kwamishinan da aka kashe, jami'ai sun cafke mutum daya

Gwamna Aminu Masari
Yanzu-Yanzu: Gwamnati ta buɗe hanyoyin sadarwa da aka datse a jihar Katsina Hoto: punchng.com
Asali: UGC

Babban mai baiwa gwamna Masari shawara ta musamman kan harkokin tsaro, Ibrahim Muhammad Katsina, shine ya faɗi haka a wata sanarwa da ya fitar.

Meyasa za'a dawo da sabis Katsina?

Bayan shafe watanni uku da rufe hanyoyin sadarwa a kananan hukumomi 17, da rufe wasu kasuwanni, wanda gwamnatin jihar Katsina ta yi, ta bada umarnin sake bude su.

A cewar hadimin gwamna, gwamnatin Katsina ta ɗauki wannan matakin ne bayan gano cewa an samu saukin ayyukan ta'addancin yan bindiga da kuma masu kwarmata musu bayanai.

Yace:

"Gwamnati ta datse hanyoyin sadarwa ne na wani lokaci, da nufin dakile ayyukan yan bindiga da masu taimaka musu da bayanai, musamman a waɗan nan kananan hukumomi 17."

Daga ƙarshe, Mashawarcin gwamnan ya yi kira ga Katsinawa su cigaba da baiwa gwamnati goyon baya a kokarinta na ganin ta magance matsalar tsaron da ta addabi jihar.

Kara karanta wannan

Uwargida ta waskawa miji mari ana tsakiyar shirin ma'aurata a gidan Rediyo, bidiyo

A wani labarin na daban kuma bayan hatsarin kwalekwale da ya faru a Kano, Gwamnatin Ganduje ta dakatar da sufurin jiragen ruwa a Bagwai

Gwamnatin Kano ta sanar da ɗaukar matakin dakatar da sufurin jiragen ruwa a yankin karamar hukumar Bagwai.

Rahoto ya nuna cewa a zaman majalisar zartarwa, gwamnatin ta kafa kwamitin da zai binciko musabbabin hatsarin da ya lakume sama da rai 20.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262