Da dumi-dumi: Gobara ta sake tashi a wata kasuwar Abuja

Da dumi-dumi: Gobara ta sake tashi a wata kasuwar Abuja

  • An samu tashin gobara a kasuwar Nyanya da ke babbar birnin tarayya, Abuja, a daren ranar Talata, 23 ga watan Nuwamba
  • Zuwa yanzu ba a san musababbin gobarar ba amma jami'an hukumar kashe gobara ta birnin tarayya na nan suna aikin saisaita annobar
  • Hakazalika ba a rasa rai ba a gobarar wacce ta fara ci da karfe 8:00 na daren nan

Birnin tarayya, Abuja - Gobara ta tashi a kasuwar Nyanya da ke babbar birnin tarayya, Abuja, a daren ranar Talata, 23 ga watan Nuwamba, jaridar Vanguard ta rahoto.

Lamarin na zuwa ne kimanin makonni uku bayan gobara ta lakume akalla rayuka goma a shahararriyar kasuwar nan ta Kubwa.

Da dumi-dumi: Gobara ta sake tashi a wata kasuwar Abuja
Da dumi-dumi: Gobara ta sake tashi a wata kasuwar Abuja Hoto: dailytrust.com
Asali: Facebook

An tattaro cewa ba a san abun da ya haddasa gobarar ba wacce ta fara da misalin karfe 8:00 na dare, kuma ba a rasa rai ba a daidai lokacin kawo wannan rahoton.

Kara karanta wannan

Kano: Gagarumar gobara ta kurmushe a kalla shaguna 41 a kasuwar Kurmi

Tuni aka zuba jami’an hukumar kashe gobara ta birnin tarayya domin daidaita annobar.

A ruwayar gidan talbijin na AIT, an gano masu kashe gobara na zarya zuwa wajen afkuwar lamarin a babban titin Abuja-Keffi.

Kano: Gagarumar gobara ta kurmushe a kalla shaguna 41 a kasuwar Kurmi

A wani labari makamancin haka, mun kawo a baya cewa a kalla shaguna 41 ne suka kurmushe sakamakon gagarumar gobarar da ta tashi a fitacciyar kasuwar Kurmi ta jihar Knao a ranar Litinin, hukumar kashe gobara ta sanar.

Daily Trust ta ruwaito cewa, Kurmi ta na daya daga cikin tsofaffin kasuwannin da ke garin Kano, cibiyar kasuwancin arewacin Najeriya.

Iblitala'in wanda ya fara wurin karfe 2 na dare, ya shafi shagunan masu siyar da litattafai a kasuwar.

Kara karanta wannan

Rahoto: Yadda aka hallaka mutane 52 a Sokoto cikin kwanaki biyu kacal

Kamar yadda mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar, Alhaji Saminu Abdullahi yace:

"Mun samu kiran gaggawa daga wani Malam Baba Nasidi wurin karfe daya da minti hamsin da takwas na dare kan cewa gobara ta tashi a kasuwar litattafai.
"Bayan samun bayanin, mun gaggauta aika masu kashe gobara zuwa wurin inda suka isa karfe biyu da minti bakwai domin kashe gobarar."

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng