Jarumar Fim da Bidiyon Tsiraicinta Ya Bazu a Intanet Ta Yi Magana

Jarumar Fim da Bidiyon Tsiraicinta Ya Bazu a Intanet Ta Yi Magana

  • Fitacciyar jarumar fina-finan Nollywood, Moyo Lawal, ta bayyana yadda bidiyon tsiraicinta da ya fita ya yi mata mummunan tasiri a rayuwa
  • Ta ce ta ɗauki hutu domin samawa kanta sauki, yin nazari a kan rayuwa da kuma fara sabon babi mai cike da natsuwa da sauyin dabi’u
  • Jarumar ta kuma jaddada cewa an dauki bidiyon da ya fita ne yardarta a wancan lokacin, amma ba tare da izininta ba aka yada shi a duniya ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Fitacciyar jarumar fina-finan Najeriya, Moyo Lawal, ta sake bayyana yadda fitar bidiyon tsiraicinta a baya ya sauya yanayin rayuwarta gaba ɗaya, musamman a ɓangaren tunani.

Ta ce bidiyon tsiraicinta da ya bazu a kafafen sada zumunta a shekarar 2023 ya jefa ta cikin matsanancin hali da kuncin rayuwa sosai.

Kara karanta wannan

Sheikh Isa Pantami ya yi magana kan rade radin cewa zai auri Aisha Buhari

Jarumar fina-finai, Moyo Lawal
Fitacciyar jarumar fim a Najeriya, Moyo Lawal. Hoto: @moyolawal
Source: Twitter

Vanguard ta wallafa cewa Moyo Lawal, wadda aka sani da kwarin gwiwa da fara’a a bainar jama’a, ta bayyana cewa lamarin ya sa ta ji rauni matuƙa, har ta yanke shawarar janyewa daga shiga jama’a da kafafen sada zumunta.

Tasirin bidiyon tsiraicin jarumar fim

A wani rubutu da ta wallafa a bikin zagayowar ranar haihuwarta, 1, Janairu, 2026, jarumar ta ce ta tsinci kanta a wani sabon babi na rayuwa, inda ta fi mai da hankali kan gyaran hali da sake tsara manufar rayuwarta.

A bayanin da ta yi, Moyo Lawal ta bayyana cewa bidiyon da ya fita ya yi mata mummunan tasiri a ɓangaren lafiyar kwakwalwa da zuciya.

Ta ce lokacin ne karo na farko da ta ji rauni da gazawa a rayuwa, abin da ya sa ta fahimci cewa samun mafita na zuwa ta hanyoyi daban-daban.

Jarumar fim a Najeriya, Moyo Lawal
Fitacciyar jarumar fim, Moyo Lawal. Hoto: @moyolawal
Source: Instagram

Jarumar ta kara da cewa lokacin da ta shafe tana nesa da jama’a ya kasance mai muhimmanci, domin ya ba ta damar yin nazari a kan rayuwarta, fahimtar kura-kuranta.

Kara karanta wannan

ADC na zuga Tinubu ya cire tsoro ya yi martani kan harin Trump a Venezuela

Martanin masu sukar Moyo a Intanet

Bayan fitar bidiyon, ra’ayoyin jama’a sun kasu gida-gida. Wasu sun nuna mata goyon baya da tausayi, yayin da wasu kuma suka ɗaura mata alhakin abin da ya faru, suna sukar yadda take yawan bayyana kanta a kafafen sada zumunta.

Sai dai jarumar ta bayyana cewa sukar da aka yi mata ya ƙara mata damuwa a zuciya, amma a ƙarshe ta koyi ware abin da zai taimaka mata daga abin da zai ƙara mata raɗaɗi.

Moyo Lawal ta yi barazana daukar mataki

A wani rahoton da BBC ta wallafa a shekarar 2023, lokacin da bidiyon ya fita, Moyo Lawal ta yi barazanar ɗaukar matakin doka.

Ta jaddada cewa bidiyon na sirri ne, an ɗauke shi ne a cikin alakar soyayya a wancan lokacin, ba don ya shiga idon jama’a ba.

Moyo Lawal ta musanta jita-jitar da ke cewa ita ce ta saki bidiyon da gangan, tana mai cewa watsa bidiyon ba tare da izininta ba babban laifi ne.

Kara karanta wannan

Yunkurin juyin mulki: Yadda sojoji suka kama Shehin malami, Khalifa Zariya a Abuja

Auren jarumar fim a Najeriya ya mutu

A wani labarin, kun ji cewa fitacciyar jarumar fim, Anita Joseph ta sanar da mutuwar aurenta da MC Fish Michael a wani sako da ta fitar.

A sanarwar da ta fitar, jarumar ta bayyana cewa bata da lokacin amsa wasu tambayoyi game da wadanda za su yi magana a kan lamarin.

Maganar da Anita Joseph ta yi ya kawo karshen rade-radin da aka shafe lokaci ana yi a kafafen sada zumunta game da aurenta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng