Kasar Iran Ta Amince Za Ta Tura Tawaga, Ta Bayyana Abin da Za Ta Gabatar ga Amurka
- Iran ta tabbatar da cewa za ta tura tawagar wakilanta zuwa wurin da aka tanada domin tattaunawa da Amurka da Isra'ila
- Jakadan Iran a kasar Pakistan, Reza Amiri Moghadam ya bayyana cewa tawagar kasarsa za ta isa birnin Islamabad yau Alhamis
- Ya nuna cewa akwai rashin amincewa a tsakanin ‘yan Iran, musamman saboda zargin cewa Isra’ila na ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita wuta
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Pakistan - Jakadan kasar Musulunci ta Iran a Pakistan, Reza Amiri Moghadam, ya sanar cewa wata tawaga daga kasarsa za ta isa birnin Islamabad a daren yau Alhamis, 9 ga watan Afrilun 2026.
Moghadam ya ce Iran za ta tura tawaga zuwa Pakistan ne domin tattaunawa kan yadda za a warware rikicin da ke tsakaninta da Amurka da Isra’ila.

Kara karanta wannan
Ana wata ga wata: Amurka ta karya sharudda 3 daga cikin yarjejeniyar sulhu da kasar Iran

Source: Twitter
Tawagar Iran ta nufi kasar Pakistan
Jakadan ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X da safiyar yau yayin da aka fara nuna wa juna yatsa tsakanin Iran da Amurka kan ci gaba da kai hare-hare Lebanon.
Iran ta fito fili ta yi Allah wadai da sababbin hare-haren da Isra'ila ta kai kasar Lebanon a jiya Laraba duk da yarjejeniyar da aka yi ta tsagaita wuta.
Hakan dai ya sa aka fara fargabar yiwuwar Iran ta janye daga tattaunawar da aka shirya a Islamabad bayan ta yi barazanar ficewa daga yarjejeniyar tsagaita wuta muddin Isra'ila ta ci gaba da kai farmaki Lebanon.
Sai dai jakadan Iran a Pakistan, Moghadam ya warware wannan fargaba, inda ya ce tawagar Iran za ta isa wurin tattaunawar a yau Alhamis.
Abubuwan da za a tattauna a taron
A cewar jakadan, tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan sharudda 10 da Iran ta gabatar a matsayin hanyar samar da mafita ga rikicin.

Kara karanta wannan
Tun ba a je ko'ina ba, Shugaba Trump ya canza tsarin tattaunawar Amurka da kasar Iran
Moghadam ya ce:
“Duk da shakku da ra’ayoyin jama’ar Iran ke da shi sakamakon yadda Isra’ila ke karya yarjejeniyar tsagaita wuta, tawagar Iran za ta isa birnin Islamabad yau domin gudanar da tattaunawa mai muhimmanci bisa sharudda 10 da Iran ta gabatar.”

Source: Getty Images
Mutanen kasar Iran sun fusata
Jakadan ya nuna cewa akwai rashin amincewa a tsakanin ‘yan Iran, musamman saboda zargin cewa Isra’ila na ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma a baya, cewar rahoton Reuters.
Wannan shakku na iya shafar yadda tattaunawar za ta gudana, duk da cewa gwamnatin Iran ta nuna aniyarta na ci gaba da neman mafita ta hanyar diflomasiyya.
Sharuddan da ake zargin Amurka ta karya
A wani rahoton, kun ji cewa Shugaban Majalisar Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf ya lissafa sharudda uku da yake zargin Amurka ta karya a yarjejeniyar tsagaita wuta.
Wannan zargi dai na zuwa ne kasa da kwana guda bayan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin da ke yaki a Gabas ta Tsakiya.
Ghalibaf ya bayyana cewa irin wannan hali na kara tabbatar da rashin amincewar da Iran ke yi wa Amurka tun shekaru da dama da suka shige.
Asali: Legit.ng