Kanada Ta Gano Masu Laifi a Yakin da Ya Barke tsakanin Amurka, Isra'ila da Iran
- Kasar Kanada ta tsoma baki kan yakin da ya barke tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kasashen Amurka da Isra'ila
- Firaministan Kanada, Mark Carney ya ce hare-haren da Amurka da Isra'ila suka fara kai wa Iran ya saba wa dokokin kasa da kasa
- Wannan na zuwa ne yayin da aka shiga rana ta biyar da fara musayar wuta tsakanin kasashen, lamarin da ya jawo asarar rayuka
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Canada - Firaministan Canada, Mark Carney, ya bayyana cewa hare-haren hadin gwiwa da Amurka da Isra'ila suka kai wa Iran ya saba wa dokar kasa da kasa ta duniya.
Carney ya yi wannan bayani ne yayin wani taro da Lowy Institute ta shirya a birnin Sydney na kasar Australia.

Source: Getty Images
A rahoton da Leadership ta kawo, Firaministan ya ce Kanada na maraba da duk wani yunkuri da zai kawo sauyi a tsarin mulkin Iran, wanda ya bayyana a matsayin tushen rashin zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.
Kanada ta yi magana kan yakin Iran
Sai dai ya ce duk da Kanada na son a samu sauyin gwamnati a Iran, amma a zahiri hare-haren da Amurka da Isra'ila suka kai mata ba su yi daidai da ka’idojin dokokin kasa da kasa ba.
“A ganina, abin bai da alaka da dokokin kasa da kasa, amma hukuncin karshe na hannun kwararrun masana. Ni ba lauya ba ne, balle kuma kwararre a dokokin kasa da kasa.”
Wannan furuci nasa ya zo ne a rana ta biyu na ziyararsa a Australia, a wani bangare na rangadin yankin Asia-Pacific domin jawo zuba jari da kuma karfafa alaka da kasashen da ake kira masu matsakaicin karfi.
Ya ce rangadin na da nufin rage dogaro da Amurka, musamman yayin da yake gargadin cewa tsarin duniya da Amurka ke jagoranta na fuskantar rauni.
Abin da ya hada Kanada da Shugaba Trump
Carney, ya sha yin sukar Shugaban Amurka Donald Trump, wanda ya taba yin barazanar hade Canada da Amurka tare da kakaba wa kayayyakin Kanada haraji mai tsanani.
A ranar Laraba, ya bayyana rikicin Gabas ta Tsakiya a matsayin wani misali na gazawar tsarin kasa da kasa, yana mai sake kira ga kaasashen duniya da su zauna lafiya.
“Canada na kira da a dakatar da tashin hankali cikin gaggawa kuma a shirye take ta taimaka wajen cimma hakan,” in ji shi.

Source: Twitter
Ya kuma soki rashin tuntubar kungiyoyin kasa da kasa, yana mai cewa Amurka da Isra’ila sun dauki mataki bisa ra'ayin kansu ba tare da tuntubar Majalisar dinkin duniya ba, cewar rahoton Gulf News
Iran ta jawo wa Amurka babbar asara
A wani rahoton, kun ji cewa an kiyasta cewa kasar Amurka ta yi asarar kayan aikin soja da kudinsu ya kai kusan Dala biliyan 1.9 sakamakon hare-haren Iran.
Alkaluman kididdigar da aka tattara sun nuna cewa hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kaddamar sun janyo babbar asara ga kadarorin sojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.
Iran ta kai hari kan sansanonin soja da ofisoshin jakadancin Amurka a kasashe da dama na Gabas ta Tsakiya bayan harin da aka kai mata, lamarin da ya jawowa Amurka asara.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

