Ba a Gama da Iran ba, Amurka Ta Kaddamar da Hare Hare a Kasar Ecuador
- Rundunar sojin Amurka sun kaddamar da sababbin hare-hare a wani yanki na kasar Ecuador kamar yadda ta sanar a ranar Talata, 3 ga Fabrairun 2026
- Hakan na zuwa ne yayin da ake cigaba da gwabza yaki da Iran da Amurka/Isra'ila a yankin Gabas ta Tsakiya bayan kashe Ayotollah Ali Khamenei
- Gwamnatin kasar Ecuador ta yi magana bayan harin kamar yadda kwanmandan sojojin Amurka ya yi karin haske ga manema labarai a wata sanarwa
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Ecuador - Sojojin Amurka da na Ecuador sun fara kai farmakin hadin gwiwa domin yaki da safarar miyagun kwayoyi a wasu yankuna.
Rundunar sojin Amurka ta bayyana cewa ta kai wani farmaki a ranar Talata a Ecuador, sai dai bangarorin biyu ba su bayar da karin bayani ba.

Source: Getty Images
Amurka ta kai hari kasar Ecuador
The Guardian ta rahoto cewa rundunar Amurka da ke kula da kasashe 31 a yankin Caribbean da sauransu ta sanar da kai hari wani yanki na Ecuardor.
A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin X, rundunar sojin Amurka ta bayyana harin a matsayin “mataki mai karfi” da ke da nufin yaki da safarar miyagun kwayoyi ba bisa ka’ida ba.
Amurka ta ce ta kai harin ne tare da hadin gwiwar Ecuador:
“Muna ɗaukar mataki mai ƙarfi tare domin fuskantar ‘yan ta’adda, waɗanda suka daɗe suna haddasa tsoro, tashin hankali da rashawa ga al’ummar yankin nahiyar nan."
Kwamandan rundunar, Janar Francis L. Donovan ya kara da cewa:
“Mun yaba wa maza da mata na rundunar sojin Ecuador bisa jajircewarsu a wannan fafutuka, inda suke nuna jaruntaka ta hanyar ci gaba da ɗaukar matakai kan ‘yan ta’adda a ƙasarsu.”
Bayanin kasar Ecuador kan harin
Bayan kai farmakin, ma’aikatar tsaron kasar Ecuador ta ce ba za ta yi cikakken bayani kan hare-haren da ake kaiwa kan 'yan ta'addan ba.
Sanarwar ta zo ne kwana guda bayan kasar da ke Kudancin Amurka ta ce Washington ya shiga wani “sabon mataki” a abin da ta kira yaki da miyagun kwayoyi.
Shugaban Ecuador, Daniel Noboa, wanda ake ganin na kusa da Donald Trump ne, ya ce Washington na daga cikin kawayen yankin da ke shiga aikin yaki da kungiyoyin safarar miyagun kwayoyi.

Source: Getty Images
A ranar Litinin, Noboa ya gana da shugaban rundunar, Francis Donovan da kuma shugaban rundunar ayyuka na musamman a yankin, Mark Schafer.
A yayin ganawar, sun tattauna shirye-shiryen musayar bayanai da daidaita ayyuka a filayen jiragen sama da tashoshin jiragen ruwa, kamar yadda ofishin Noboa ya bayyana a wata sanarwa.
Ga bidiyon da dakarun na Amurka ta fitar kan harin:
Amurka na sabon shiri kan Iran
A wani labarin, kun ji cewa, ana zargin Shugaban Amurka, Donald Trump ya fara sabon shiri domin tunkarar kasar Iran ta bayan fage.
Wasu rahotanni sun ce Trump na tattaunawa da shugabannin Kurdawa da ke dauke da makamai a Iran kan yadda za su hargitsa kasar.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake gwabza yaki tsakain Amurka da Iran bayan wani hari da Trump ya kai tare da goyon bayan Isra'ila.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


