Iran Ta Dauki Manyan Matakai 3 bayan Amurka Ta Kashe Jagoran Musulunci, Khamenei

Iran Ta Dauki Manyan Matakai 3 bayan Amurka Ta Kashe Jagoran Musulunci, Khamenei

Iran - Bayan tabbatar da mutuwar Ayatollah Ali Khamenei, sakamakon hare-haren haɗin gwiwa na Amurka da Isra'ila a ranar 28 ga Fabrairu, 2026, gwamnatin Iran ta dauki wasu tsauraran matakai.

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Imam Ayotallah Khamenei, wanda ya rasu yana ɗan shekara 86, ya kasance jagoran ƙasar tun shekarar 1989.

Iran ta dauki wasu tsauraran matakai bayan mutuwar Ayotallah Khamenei
Jagoran addinin Musulunci na Iran yana dagawa magoya bayansa hannu a Tehran. Hoto: @khamenei_ir
Source: Twitter

An tabbatar da mutuwar Khamenei

Kafar wata labarai ta NBC News ta rahoto kamfanin dillancin labaran gwamnatin Iran yana cewa:

"Ana sanar da al'ummar Iran cewa, Ayatollah Khamenei, jagoran addinin Musulunci, ya yi shahada a wani harin haɗin gwiwa da la'ananniyar ƙasar Amurka da kuma haramtacciyar ƙasar Isra'ila suka kai."

Sanarwar ta ci gaba da cewa:

"Wannan babban malami kuma gwarzon mayaƙi ya sadaukar da rayuwarsa domin ɗaukakar Iran da Musulunci, kuma insha Allahu, yana tare da Imam (Khomeini) da Shugaban Shahidai (Imam Hussain)".

Kara karanta wannan

Jagoran Musulunci na Iran: Mutane 5 da za su iya maye gurbin Ayotallah Khamenei

Shafin Telegram na gidan talabijin na ƙasar, IRIB, shi ma ya tabbatar da wannan labari, inda ya ce:

"Jagoran al'umma, jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Mai Girma Ayatollah Khamenei, ya yi shahada."

Manyan matakai 3 da Iran ta dauka

Ga matakai guda uku da Iran ta dauka bayan kisan Khamenei:

1. Zaman makoki da hutun jama'a

Kafafen yaɗa labaran gwamnatin Iran sun sanar da dokar yin zaman makoki na kwanaki 40 a faɗin ƙasar domin girmama Khamenei.

Wannan mataki ya haɗa da bayar da hutun kwanaki bakwai a jere, inda aka rufe dukkan ofisoshin gwamnati, makarantu, da wuraren kasuwanci, in ji rahoton The Business Standard.

Gidan talabijin na ƙasar ya nuna sanarwar tare da bayyana mutuwarsa a matsayin "shahada," inda aka yi kira ga jama'a da su kiyaye wannan lokaci.

2. Tsarin miƙa ragamar shugabanci

Dangane da tanadin kundin tsarin mulkin Iran, an kafa wata majalisar shugabanci domin jan ragamar ƙasar a wannan lokaci da ake shirin sauya shugaba.

Wannan hukuma mai mambobi uku ta haɗa da:

Kara karanta wannan

Rundunar Iran ta IRCG ta lashi takobin ɗaukar fansa kan kisan khamenei

  • Shugaba Masoud Pezeshkian.
  • Shugaban sashin shari'a na ƙasa.
  • Wani babban malami daga majalisar Guardian Council.

An ɗora wa wannan majalisa nauyin tabbatar da zaman lafiya da lura da harkokin yau da kullum har sai majalisar kwararru ta zaɓi sabon babban jagora, in ji rahoton Aljazeera.

An riga an fara tsarin zaɓen magajin Khamenei, kodayake ba a bayyana takamaiman lokacin da za a kammala ba saboda matsalolin tsaro.

Imam Ayotallah Ali Khamenei ya mutu ne sakamakon hare-haren Amurka da Isra'ila.
Ayotallah Khamenei, jagoran Musulunci na Iran ya gana da kwamitin shirya gasar AlKur'ani karo na 40. Hoto: @khamenei_ir
Source: Twitter

3. Matakan tsaro da harin ramuwar gayya

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun fito fili sun ɗora wa Amurka da Isra'ila alhakin harin, inda suka yi rantsuwar daukar fansa ta hanyar kai hare-hare masu tsanani.

Tuni dai Iran ta ƙaddamar da hare-haren makami mai linzami kan wasu wurare a Isra'ila da ƙasashen Gulf jim kaɗan bayan tabbatar da mutuwar Khamenei, in ji rahoton KGNS News.

A cikin gida kuma, hukumomi sun tsaurara tsaro, inda aka tura dakarun IRGC domin murƙushe zanga-zanga da kiyaye doka a daidai lokacin da ake samun hatsaniya da kuma bukukuwan murna a wasu yankuna.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Amurka da Isra'ila sun kashe jagoran addinin Musulunci na Iran

An kuma yanke intanet a faɗin ƙasar domin taƙaita sadarwa tsakanin masu adawa da gwamnati.

An kashe Ayotallah Khamenei a Iran

Tun da fari, mun ruwaito cewa, Iran ta tabbatar da kisan jagoran Musulunci, Ayatollah Ali Khamenei sakamakon harin hadin gwiwa na Amurka da Isra'ila.

An kashe jagoran ne a ofishinsa dake rukunin Beit Rahbari yayin da yake gudanar da ayyukansa na yau da kullum a ranar Asabar.

Iran za ta gudanar da zaman makokin kwanaki 40 yayin da Isra'ila ta kaddamar da sababbin hare-hare kan makaman linzamin kasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com