'Za Mu Farmaki Sansanonin Amurka,' Iran Ta Yi Babbar Barazana bayan Kalaman Trump

'Za Mu Farmaki Sansanonin Amurka,' Iran Ta Yi Babbar Barazana bayan Kalaman Trump

  • Ministan Iran Abbas Araghchi ya yi gargadin cewa za su kai hari kan sansanonin Amurka idan har Donald Trump ya farmake su
  • Tattaunawar nukiliya da aka yi a kasar Oman ta nuna alamun nasara duk da cewa Iran ta ki amincewa da tattaunawa a wasu batutuwa
  • Amurka ta taba lalata cibiyoyin nukiliyar Iran a yayin da Tehran ta maida martani ta hanyar harba makamai sansanin Amurka a Qatar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Iran - Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya yi gargaɗin cewa Tehran za ta kai hari kan sansanonin Amurka dake yankin Gabas ta Tsakiya.

Wannan martani ya biyo bayan barazanar da Shugaba Donald Trump ya yi na amfani da ƙarfin soja kan ƙasar ta Iran a kwanan nan.

Iran ta yi barazanar kai hari sansanonin Amurka da ke a Gabas ta Tsakiya.
Jirgin yaki kirar RAAF F-18 Super Hornet yana shawagi a samaniya yayin wani wasan kasa da kasa na Avalon. SOPA Images / Contributor
Source: Getty Images

Iran na barazanar farmakar sansanonin Amurka

Kara karanta wannan

Barazanar yaki: Trump ya bayyan yadda tattaunawar Amurka da Iran ta kasance

Araghchi ya bayyana cewa ba zai yiwu su kai hari cikin ƙasar Amurka ba, amma dukkan sansanoninta dake maƙwabta suna cikin haɗari, in ji rahoton Reuters.

Ya jaddada cewa Iran ba za ta kai wa ƙasashen maƙwabta hari ba, face dai sansanonin Amurka dake jibge a cikin waɗannan ƙasashe.

Ministan ya bayyana tattaunawar nukiliya da aka yi a Oman a matsayin "kyakkyawan farawa" duk da ƙaruwar zaman ɗar-ɗar a yankin.

Amurka ta buƙaci Iran ta dakatar da tace sinadarin uranium, ta taƙaita makaman ballistic, sannan ta daina tallafa wa ƙungiyoyin dake yaƙi.

Iran ta sha musanta cewa tana kera makamin nukiliya, tana mai cewa shirinta na zaman lafiya ne kawai, kuma ba za ta tattauna wasu batutuwan ba.

Araghchi ya yi watsi da yunƙurin faɗaɗa tattaunawar zuwa wasu batutuwa daban, yana mai cewa batun nukiliya ne kawai za su tattauna.

Tarihin hare-hare tsakanin Amurka da Iran

A watan Yunin da ya gabata, Amurka ta kai hari kan cibiyoyin nukiliyar Iran a cikin wani farmaki da aka yi wa laƙabi da "Operation Midnight Hammer."

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya kausasa harshe kan harin 'yan ta'adda a Kwara, ya dauki mataki

Wannan farmakin ya faru ne a kwanakin ƙarshe na harin sama da Isra'ila ta kai wa Iran na tsawon kwanaki 12 a jere.

Iran ta mayar da martani ta hanyar harba makamai masu linzami zuwa sansanin Al-Udeid na Amurka dake ƙasar Qatar a wancan lokacin, in ji rahoton Fox News.

Shugaba Donald Trump ya siffanta martanin Iran a matsayin "mai rauni sosai," inda ya ce sun kakkabo kusan dukkan makaman da aka harba.

Iran da Amurka sun fara tattaunawa sulhu a kasar Oman
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi (hagu) ya hadu da ministan harkokin wajen Oman Sayyid Badr Hamad Al Busaidi (dama) Handout/Anadolu via Getty Images
Source: Getty Images

Tattaunawar diflomasiyya a Oman

Ministan Harkokin Wajen Oman, Badr al-Busaidi, ya gana da jami'an Iran da na Amurka daban-daban a ranar Juma'ar da ta gabata.

Al-Busaidi ya gana da Araghchi, sa'an nan ya gana da wakilin Amurka Steve Witkoff da kuma Jared Kushner domin samar da maslaha.

Oman ta bayyana cewa tattaunawar ta fi mayar da hankali ne wajen samar da yanayin da zai ba da damar ci gaba da tattaunawar fasaha.

Dukkan ɓangarorin suna da muradin tabbatar da nasarar tattaunawar domin samar da tsaro da kuma zaman lafiya mai dorewa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Kara karanta wannan

Turkiyya ta shirya taimakon Najeriya bayan kisan Musulmi kusan 200 a Kwara

Ci gaban wannan tattaunawa ya dogara ne kan shawarwarin da kowane jami'i zai samu daga babban birnin ƙasarsa kafin ɗaukar mataki na gaba.

Tattaunawar Amurka da Iran

A wani labari, mun ruwaito cewa, shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya yi magana kan tattaunawar da kasarsa ta fara da Iran.

Trump ya ce Washington ta yi “tattaunawa mai kyau” da Iran bayan ɓangarorin biyu sun gudanar da tattaunawa a kasar Oman.

Iran ta ce tana sa ran ci gaba da tattaunawa da Amurka, tana mai yabawa abin da ta kira “kyakkyawan yanayi” da aka samu a ranar tattaunawar da aka yi a ƙasar Oman.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com