Hannayen Jarin Kamfanonin Faransa Sun Fadi Bayan Juyin Mulki A Gabon
- A safiyar yau Laraba aka wayi gari da labarin juyin mulki a kasar Gabon jim kadan bayan sanar da sakamakon zabe
- Dalilin juyin mulkin, kamfanonin Faransa manya-manya guda uku sun gamu da jarrabawar karyewar hannun jari
- Kamfanonin uku sun hada da Maurel/Prom, Eramet, da reshen TotalEnergies da ke kasar Gabon
DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!
Gabon - Bayan kifar da gwamnatin Ali Bongo a kasar Gabon, Faransa ta tafka mummunan asara a kasar.
Rahotanni sun tabbatar cewa hannayen jarin kamfanonin Faransa uku sun fadi a kasuwar hada-hadar hannun jari ta Paris.

Source: Facebook
Me ya jawo wa Faransa asara a Gabon?
Hakan ya faru ne a yau Laraba 30 ga watan Agusta bayan sojoji sun sanar da kifar da gwamnati a Gabon.
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kara karanta wannan
Juyin Mulkin Gabon: Jigon APC Ya Yi Martani Kan Halin Da Ake Ciki, Ya Ce A Saurari Hakan A Wasu Kasashe
Kamfanonin na gudanar da harkokinsu ne a kasar ta Gabon kafin sanar da juyin mulkin, Yeni Safak ta tattaro.
Kamfanonin uku da abin ya shafa sun hada da Maurel/Prom, Eramet, da reshen TotalEnergies na kasar Gabon.
Kamfanonin sun fadi da kashi 15 zuwa 20, a cewar jaridar Faransa ta Les Echos.
Tun farko kamfanin hakar ma'adinai na Eramet ya sanar cewa ya dakatar da ayyukansa da kuma sufurin jiragen kasa a Gabon, cewar TRT Hausa.
Me ke faruwa a Gabon da ya shafi Faransa?
An wayi garin yau Laraba da labarin cewa wasu sojojin Gabon sun sanar a gidan talabijin inda suka yi ikirarin kifar da gwamnatin Shugaba Ali Bongo
Sanarwar tasu na zuwa ne jim kadan bayan hukumar zaben kasar ta ayyana Shugaba Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben karo na uku.
Ali Bongo ya samu har kashi 64.27 na kuri'un da aka kada a ranar Asabar 26 ga watan Agusta.
Wannan juyin mulki ya kawo karshen shekaru 53 da ahalin gidan Bongo ke rike da madafun ikon kasar.

Kara karanta wannan
Yanzu Yanzu: Bikin Murna Ya Barke a Gabon Yayin da Sojoji Suka Karbe Mulki Daga Shugaban Kasa Ali Bongo, Hotuna Sun Bayyana
Ali Bongo ya dare karagar mulki a shekarar 2009 bayan rasuwar mahaifinsa Omar Bongo da ya shafe shekaru da dama a kan karagar mulki.
Sojoji Sun Kifar Da Gwamnatin Bongo A Gabon
A wani labarin, an wayi gari yau da labarin cewa sojojin kasar Gabon sun kifar da Shugaba Ali Bongo.
Wannan na zuwa ne bayan kammala zaben da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata.
Asali: Legit.ng