Hannayen Jarin Kamfanonin Faransa Sun Fadi Bayan Juyin Mulki A Gabon

Hannayen Jarin Kamfanonin Faransa Sun Fadi Bayan Juyin Mulki A Gabon

  • A safiyar yau Laraba aka wayi gari da labarin juyin mulki a kasar Gabon jim kadan bayan sanar da sakamakon zabe
  • Dalilin juyin mulkin, kamfanonin Faransa manya-manya guda uku sun gamu da jarrabawar karyewar hannun jari
  • Kamfanonin uku sun hada da Maurel/Prom, Eramet, da reshen TotalEnergies da ke kasar Gabon

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Gabon - Bayan kifar da gwamnatin Ali Bongo a kasar Gabon, Faransa ta tafka mummunan asara a kasar.

Rahotanni sun tabbatar cewa hannayen jarin kamfanonin Faransa uku sun fadi a kasuwar hada-hadar hannun jari ta Paris.

Faransa ta tafka asara bayan kifar da gwamnatin Ali Bongo
Yadda Kamfanonin Faransa Su Ka Tafka Asara A Gabon. Hoto: Emmanuel Macron, Ali Bongo.
Source: Facebook

Me ya jawo wa Faransa asara a Gabon?

Hakan ya faru ne a yau Laraba 30 ga watan Agusta bayan sojoji sun sanar da kifar da gwamnati a Gabon.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kara karanta wannan

Juyin Mulkin Gabon: Jigon APC Ya Yi Martani Kan Halin Da Ake Ciki, Ya Ce A Saurari Hakan A Wasu Kasashe

Kamfanonin na gudanar da harkokinsu ne a kasar ta Gabon kafin sanar da juyin mulkin, Yeni Safak ta tattaro.

Kamfanonin uku da abin ya shafa sun hada da Maurel/Prom, Eramet, da reshen TotalEnergies na kasar Gabon.

Kamfanonin sun fadi da kashi 15 zuwa 20, a cewar jaridar Faransa ta Les Echos.

Tun farko kamfanin hakar ma'adinai na Eramet ya sanar cewa ya dakatar da ayyukansa da kuma sufurin jiragen kasa a Gabon, cewar TRT Hausa.

Me ke faruwa a Gabon da ya shafi Faransa?

An wayi garin yau Laraba da labarin cewa wasu sojojin Gabon sun sanar a gidan talabijin inda suka yi ikirarin kifar da gwamnatin Shugaba Ali Bongo

Sanarwar tasu na zuwa ne jim kadan bayan hukumar zaben kasar ta ayyana Shugaba Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben karo na uku.

Ali Bongo ya samu har kashi 64.27 na kuri'un da aka kada a ranar Asabar 26 ga watan Agusta.

Wannan juyin mulki ya kawo karshen shekaru 53 da ahalin gidan Bongo ke rike da madafun ikon kasar.

Kara karanta wannan

Yanzu Yanzu: Bikin Murna Ya Barke a Gabon Yayin da Sojoji Suka Karbe Mulki Daga Shugaban Kasa Ali Bongo, Hotuna Sun Bayyana

Ali Bongo ya dare karagar mulki a shekarar 2009 bayan rasuwar mahaifinsa Omar Bongo da ya shafe shekaru da dama a kan karagar mulki.

Sojoji Sun Kifar Da Gwamnatin Bongo A Gabon

A wani labarin, an wayi gari yau da labarin cewa sojojin kasar Gabon sun kifar da Shugaba Ali Bongo.

Wannan na zuwa ne bayan kammala zaben da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.