Sharif Lawal
7146 articles published since 17 Fab 2023
7146 articles published since 17 Fab 2023
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta yi martani kan ficewar tsofaffin 'yan takarar shugaban kasa a zaben 2023, Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso zuwa NDC.
Tsohon gwamnan jihar Bayelsa kuma jagoran NDC na kasa, Sanata Seriake Dickson, ya warware zare da abawa kan rajistar jam'iyyar wadda ake ta shiga cikinta.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya sake yi barazana ga kasar Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Trump ya gargadi Iran kan batun tattaunawar da ake son yi.
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya nuna kwarin gwiwar cewa jam'iyyarsa ta PDP za ta samar da shugaban kasa a 2027. Makinde ya bukaci hadin kai a jam'iyyar.
Hamshakin attajiri, Femi Otedola, ya maida martani kan batun cewa ya samar da kudaden gina matatar Dangote. Attajirin ya bayyana cewa zuki ta malle ce kawai.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka wasu jagororin 'yan bindiga a Zamfara. Sojojin sun kuma hallaka wasu 'yan ta'adda tare da kwato makamai.
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ramuwar gayya a jihar Katsina. Tsagerun 'yan bindigan sun hallaka mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba.
Wasu gwamnonin da wa'adinsu zai kare a shekarar 2027 na harin tafiya majalisar dattawa. Daga cikinsu akwai gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri.
Tsohon dan takarar shugaban kasa a zaben 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya sauya sheka zuwa jam'iyyar NDC. Kwankwaso ya aika sako ga 'yan Najeriya.
Sharif Lawal
Samu kari