'Yan bindiga sun kashe mutum 10, sun raunata wasu da dama a sabon harin da suka kai Katsina
- Yan bindiga sun kai sabon hari a garin Yasore da ke kusa da Batsari a jihar Katsina
- Yayin harin, sun bindige mutum 10 har lahira, sun raunata wasu sun kona gidaje
- Wani mazaunin garin ya tabbatar da afkuwar harin inda ya ce wadanda suka jikkata suna asibiti
Katsina - 'Yan bindiga a safiyar ranar Talata sun kashe mutum 10 sun kuma raunata wasu da dama yayin sabon harin da suka kai inda suka kona shaguna da gidaje a Yasore, jihar Katsina, mazauna garin suka shaidawa Premium Times.
Yasore ba shi da nisa da Batsari, hedkwatar karamar hukumar Batsari.

Asali: Facebook
Batsari na daya daga cikin kananan hukumomin da 'yan bindiga ke yawan kai hari. Yana da iyaka da dajin Rugu, karamar hukumar Katsina da Zurmi a jihar Zamfara.
An toshe layukan sadarwa a Batsari da wasu kananan hukumomi 13 a jihar a matsayin wani mataki na magance 'yan bindiga.

Asali: Facebook
Wani mazaunin unguwar, Harisu Hamsa, ya shaida wa Premium Times cewa maharan sun taho ne a kan babura suka fara harbe-harbe.

Asali: Facebook
Ya ce:
"Sun taho lokacin sallar Magariba. Wasu sun gama salla a lokacin. Sun taho kan babura fiye da 20, a yayin harbe-harben ne suka kashe mutum 10 suka raunata wasu."
Mr Hamza wanda ke zaune a birnin Katsina ya tabbatar da cewa yan bindigan sun cinna wa wasu gidaje wuta.
A cewarsa:
"Sun sace kayan abinci da wasu kayayyakin da suke bukata a yayin harin."
Majiyar Legit.ng ta tattaro cewa an kai wadanda suka jikkata babban asibitin Katsina.

Kara karanta wannan
Miyagun yan bindiga sun bude wa masallata wuta, Sun kashe aƙalla 10 a jihar Katsina
Mai magana da yawun yan sandan jihar, Gambo Isa, ya ce yana cikin taro ne a lokacin da wakilin majiyar Legit.ng ya tuntube shi. Amma, bai amsa sakon kar ta kwana da aka aika masa ba.
Sarkin Katsina ya barranta da matsayar Sheikh Gumi: Kisa ya dace da ƴan bindiga ba tattaunawa da su ba
A wani labarin daba, mai martaba Sarkin Katsina ya ce tunda ƴan bindiga sun zaɓi su rika kashe mutane 'suma bai dace a bar su da rai ba'.
Sarkin na Katsina, Abdulmuminu Usman ya ce ba abin da ya dace da ƴan bindigan da ke kashe mutane a arewa maso yamma illa kisa.
Sarkin ya yi wannan furucin ne yayin taron tsaro na masu ruwa da tsaki a ranar Talata a Katsina kamar yadda Premium Times ta ruwaito.
Asali: Legit.ng