'Yan bindiga sun kashe mutum 10, sun raunata wasu da dama a sabon harin da suka kai Katsina

'Yan bindiga sun kashe mutum 10, sun raunata wasu da dama a sabon harin da suka kai Katsina

  • Yan bindiga sun kai sabon hari a garin Yasore da ke kusa da Batsari a jihar Katsina
  • Yayin harin, sun bindige mutum 10 har lahira, sun raunata wasu sun kona gidaje
  • Wani mazaunin garin ya tabbatar da afkuwar harin inda ya ce wadanda suka jikkata suna asibiti

Katsina - 'Yan bindiga a safiyar ranar Talata sun kashe mutum 10 sun kuma raunata wasu da dama yayin sabon harin da suka kai inda suka kona shaguna da gidaje a Yasore, jihar Katsina, mazauna garin suka shaidawa Premium Times.

Yasore ba shi da nisa da Batsari, hedkwatar karamar hukumar Batsari.

'Yan bindiga sun kashe mutum 10, sun raunata da dama a sabon harin da suka kai Katsina
Babur da 'yan bindiga suka kona a harin da suka kai Yasore. Hoto: Premium Times
Asali: Facebook

Kara karanta wannan

Hotunan kyakyawar budurwar da ta rasu ana saura kwanaki 3 auren ta

Batsari na daya daga cikin kananan hukumomin da 'yan bindiga ke yawan kai hari. Yana da iyaka da dajin Rugu, karamar hukumar Katsina da Zurmi a jihar Zamfara.

An toshe layukan sadarwa a Batsari da wasu kananan hukumomi 13 a jihar a matsayin wani mataki na magance 'yan bindiga.

'Yan bindiga sun kashe mutum 10, sun raunata da dama a sabon harin da suka kai Katsina
Hotunan barnar da yan bindiga suka yi a harin Yasore. Hoto: Premium Times
Asali: Facebook

Wani mazaunin unguwar, Harisu Hamsa, ya shaida wa Premium Times cewa maharan sun taho ne a kan babura suka fara harbe-harbe.

'Yan bindiga sun kashe mutum 10, sun raunata da dama a sabon harin da suka kai Katsina
Wuraren da 'yan bindiga suka kona a harin Yasore a Katsina. Hoto: Premium Times
Asali: Facebook

Ya ce:

"Sun taho lokacin sallar Magariba. Wasu sun gama salla a lokacin. Sun taho kan babura fiye da 20, a yayin harbe-harben ne suka kashe mutum 10 suka raunata wasu."

Mr Hamza wanda ke zaune a birnin Katsina ya tabbatar da cewa yan bindigan sun cinna wa wasu gidaje wuta.

A cewarsa:

"Sun sace kayan abinci da wasu kayayyakin da suke bukata a yayin harin."

Majiyar Legit.ng ta tattaro cewa an kai wadanda suka jikkata babban asibitin Katsina.

Kara karanta wannan

Miyagun yan bindiga sun bude wa masallata wuta, Sun kashe aƙalla 10 a jihar Katsina

Mai magana da yawun yan sandan jihar, Gambo Isa, ya ce yana cikin taro ne a lokacin da wakilin majiyar Legit.ng ya tuntube shi. Amma, bai amsa sakon kar ta kwana da aka aika masa ba.

Sarkin Katsina ya barranta da matsayar Sheikh Gumi: Kisa ya dace da ƴan bindiga ba tattaunawa da su ba

A wani labarin daba, mai martaba Sarkin Katsina ya ce tunda ƴan bindiga sun zaɓi su rika kashe mutane 'suma bai dace a bar su da rai ba'.

Sarkin na Katsina, Abdulmuminu Usman ya ce ba abin da ya dace da ƴan bindigan da ke kashe mutane a arewa maso yamma illa kisa.

Sarkin ya yi wannan furucin ne yayin taron tsaro na masu ruwa da tsaki a ranar Talata a Katsina kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

Asali: Legit.ng

Online view pixel