Don faranta wa miji na rai, na kan ba shi ɗanin mahaifiyata da ƙanwata, Matar Aure

Don faranta wa miji na rai, na kan ba shi ɗanin mahaifiyata da ƙanwata, Matar Aure

  • Wata mata ta bayyana hanyar da take bi don faranta wa mijin ta rai
  • Kamar yadda Madi Brooks ta bayyana, yadda take ba mijinta damar kwanciya da mahaifiyar ta
  • A cewar ta, ta kan ba shi damar shakatawa da ‘yar uwarta idan har ya bukaci hakan

Amurka - Wata mata ta bayyana yadda take bai wa mijin ta damar kwanciya da mahaifiyar ta da ‘yar’uwar ta.

Madi Brooks ‘yar Amurka ce ta bayyana wa mabiyan ta na TikTok wadanda sun wuce mutane 92,700 dangane da rayuwar auren ta.

Don faranta wa miji na rai, na kan ba shi ɗanin mahaifiyata da ƙanwata, Matar Aure
Don faranta wa mijina rai, na kan ba shi ɗanin mahaifiyata da ƙanwata, Matar Aure. Hoto: LIB
Asali: Facebook

Matar, mahaifiyar ta da mijin ta su na rayuwa yadda su ka ga dama, sannan har kanwar ta ma ba su bari a baya ba.

Kara karanta wannan

Ko a jikina asarar da na tafka, abu daya ne ya dame ni, Zuckerberg mai kamfanin Facebook

A bidiyon da ta wallafa kamar yadda LIB ta ruwaito, ta ce:

“Ni da mahaifiya ta mu na musayar miji na wurin kwanciya, kuma hakan ya na da kayatarwa kwarai.
“Kun san dalili? Idan na ji ba zan iya ba shi kai na ba, sai in ba shi damar kwantawa da ita.
“Eh! Ni irin matar nan ne. Ba na bai wa miji na kaina sai sau 2 a mako.”

Ta ce ya kan dana kanwar ta

Madi ta ce har kanwar ta ma ta na kwanciya da mijin ta.

Kamar yadda ta bayyana bisa ruwayar LIB:

“Idan kana so ka san yadda nake faranta wa miji na rai, ina ba shi damar kwanciya da kanwata ne."

Wallafar bidiyon ya janyo cece-kuce iri-iri. Kamar yadda wani ya yi tsokaci:

“Wannan TikTok din shekara kenan na yi, na kama gaba na."

A raba mu, ya ce na cika mugun ci, har rufe kicin yake yi da dare, Firdausi ta yi karar mijinta Haruna a kotu

Kara karanta wannan

Yobe: Mata mai juna biyu ta haɗa baki da wasu maza 2 wurin garkuwa da kanta

A wani labarin daban, a ranar Litinin wata Firdausi Sulaiman mai shekaru 23 ta maka mijin ta, Haruna Haruna a gaban kotun musulunci da ke zama a Magajin Gari a Kaduna tana bukatar a raba auren su da shi saboda yadda yake dukanta kamar gangar tashe sakamakon mungun cin abincin ta.

Kamar yadda NewsWireNGR ta bayyana, a korafin da ta yi wa Kotu, Firdausi wacce take zama a Rigasa dake Kaduna ta ce har rufe kicin Haruna yake yi da dare.

Alkalin kotun, Nuhu Falalu, bayan sauraron bangarorin guda biyu, ya dage sauraron shari’ar har sai ranar 4 ga watan Oktoba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel