Ganduje, Amaechi, Ikweremadu, wasu mutum 22 da suke cin taliyar siyasa tun 1999 har yanzu

Ganduje, Amaechi, Ikweremadu, wasu mutum 22 da suke cin taliyar siyasa tun 1999 har yanzu

  • Akwai ‘yan siyasar da tun 1999 suke rike da mukaman gwamnati har yau
  • Wadannan ‘yan siyasan suna ta canza ofis ne na tsawon shekara 22 a jere
  • Daga cikinsu akwai Ahmad Lawan, Abdullahi Ganduje, da Ali Modu Sheriff

Nigeria - Shekara 22 kenan akwai wasu ‘yan siyasa 22 a kasar nan da har yanzu suna cikin gwamnati. An cigaba da dama wa da wadannan mutane tun 1999.

Jaridar Daily Trust tayi wani bincike na musamman, ta tattaro ‘yan siyasar da har gobe ake yi da su. Tun da aka dawo mulkin farar hula dai suke rike da mukamai.

Ga ‘yan siyasar nan kamar yadda jaridar ta kawo:

1. Ahmad Lawan

A 1999 ya zama ‘dan majalisar wakilan tarayya, a 2007 aka zabe shi a matsayin Sanatan Yobe ta Arewa. Shugaban majalisar dattawa tun 2019 zuwa yanzu.

Kara karanta wannan

Sarakunan gargajiya 65 sun yi wa Asiwaju Tinubu mubaya’a ya zama Shugaban kasa a 2023

2. Danjuma Goje

Mohammed Danjuma Goje ya zama Minista a 1999, tsakanin 2003 da 2011 ya yi gwamnan jihar Gombe. Tun bayan nan ne yake Sanata a majalisar dattawa.

3. Ike Ekweremadu

Sanata Ike Ekweremadu ya shiga gwamnati tun 1997, ya rike mukamai a gwamnatin Enugu daga 1999 zuwa 2001. A 2003 ya zama Sanata, har yau yana nan.

4. Raji Fashola

Babatunde Raji Fashola yana cikin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu a 1999. A 2007 ya zama gwamnan Legas. Tun bayan nan kuma yake Minista har yau.

5. Adamu Aliero

Muhammad Adamu Aliero ya yi gwamnan Kebbi daga 1999. A 2007 ya bar Minista, ya zama Ministan Abuja. Yanzu haka ya sake koma wa majalisar dattawa.

‘Yan siyasa 22 masu dogon zamani
'Yan siyasan da suka ki cin taliyar karshe Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

6. Aliyu Wamakko

Tsohon mataimakin gwamna, tsohon gwamna, yanzu Sanata mai wakiltar Sokoto ta yamma.

Kara karanta wannan

Tsohon Kwamishina ya yi magana bayan Mai dakin Ganduje ta shiga hannun Jami'an EFCC

7. Rauf Aregbesola

Kwamishina a gwamnatin Tinubu, zuwa gwamnan Osun har 2018, yanzu yana Ministan gida.

8. Chris Ngige

Tsohon Sakataren PDP, Gwamnan Anambra a 2003, tsohon Sanata, kuma Ministan kwadago.

9. George Akume

Akume ya yi gwamna daga 1999 zuwa 2007, sai ya zama Sanata har 2019, yanzu yana Minista.

10. Rotimi Amaechi

Amaechi ya yi shugaban majalisar Ribas daga 1999, sai ya zama Gwamna, daga nan yake Minista.

Sauran ‘yan siyasar sune:

11. Enyinnaya Abaribe

12. James Manager

13. Abdullahi Umar Ganduje

14. Pauline Tallen

15. Ali Modu Sheriff

Sun yi Gwamna, yanzu suna Majalisa

Ragowar sune wadanda sun yi gwamna, yanzu suna majalisar dattawa

16. Rochas Okorocha

17. Abdullahi Adamu

18. Ibikunle Amosun

19. Orji Uzor Kalu

20. Sam Egwu

21. Ibrahim Geidam

22. Gabriel Suswam

Lissafin PDP a 2023

A makon da ya wuce ne kuka ji cewa ana tunani jam’iyyar adawa ta PDP tana shirin watsi da ‘Yan siyasan Arewa a takarar Shugaban kasan da za ayi a shekarar 2023.

Kara karanta wannan

2023: Ai ba a yin dole a siyasa – Tsohon Gwamnan Arewa ya yi wa Gwamnonin Kudu raddi

Idan aka tafi a haka, babu mamaki ‘Dan Kudu zai rike wa PDP tuta a zaben 2023. A halin yanzu an ba 'Dan Arewa dama ya fito takarar kujerar shugaban jam'iyyar PDP.

Asali: Legit.ng

Online view pixel