Bagudu: Wasu kasashen su na da wurin kiwo da ya fi girman wasu jihohin Najeriya

Bagudu: Wasu kasashen su na da wurin kiwo da ya fi girman wasu jihohin Najeriya

  • Atiku Bagudu, gwamnan jihar Kebbi ya ce akwai kasashen da ke da manyan wuraren kiwo killatattu
  • Kamar yadda ya sanar a tattaunawar da aka yi da shi a ranar Alhamis, wuraren kiwon sun fi wasu jihohi a kasar nan girma
  • Ya goyi bayan shugaban kasa Muhammadu Buhari kan umarnin da ya bada na kafa wuraren kiwo 368 a jihohi 25

Kebbi - Gwamna Atiku Bagudu na jihar Kebbi ya ce wasu kasashe suna da wuraren kiwo da suka fi wasu jihohi a Najeriya girma.

Ya sanar da hakan ne yayin tattaunawa kan rikicin makiyaya da Fulani a gidan talabijin na Channels da aka yi da shi.

A yayin kare umarnin shugaban kasa Muhammadu kan samar da wuraren kiwo a kasar nan, Bagudu ya ce dubawa tare da gane hanyoyin kiwo zai taimaka wurin shawo kan matsalar makiyaya da manoma.

Kara karanta wannan

Masu garkuwa da mutane sun kashe mace mai juna biyu a Zaria

A cikin kwanakin nan ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umarni ga kwamiti da a sake duba yadda za a samar da wuraren kiwo 368 a jihohi 25 na kasar nan.

Bagudu: Wasu kasashen su na da wurin kiwo da ya fi girman wasu jihohin Najeriya
Bagudu ya goyi bayan shugaban kasa Muhammadu Buhari wurin kafa wuraren kiwo a kasar nan. Hoto daga dailytrust.com
Asali: UGC

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, wannan ya faru ne har da jajircewar wasu bangarori na kasar. Amma Bagudu ya ce umarnin shugaban kasan bai hana kiwon ba kwata-kwata.

"Kwamitin zai duba hanyoyin kiwo kuma ya yi aiki da jihohi wurin gina su. Hakan zai sa a gano yawan matsalar."
"Shugaban kasan ya na da ra'ayi wurin duba wuraren kiwo. Aiki ne na sa kai kuma dole ne a hada kai da jihohi. Jama'a na cewa mun yi magana kan kiwo. Tabbas, amma mene ne wurin kiwo? Ba a kiwo a iska, ana yin shi ne a fili.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Buhari ta yi nasarar kwato N1trn na kudin sata, Shugabannin APC

"A wasu kasashen kamar su Australia, wuraren kiwo sun fi wasu jihohin Najeriya girma. Toh don haka ta yaya ake gane abinda akwai? Ya ya za a yi a zamanantar da su?

Bagudu: Muguntar 'yan bindiga ta fi shafar Fulani, ba mu sauraron labaransu ne kawai

A wani labari na daban, Atiku Bagudu, gwamnan jihar Kebbi, ya ce matsalar garkuwa da mutane tare da satar shanu a kasar nan ta fi shafar Fulani.

A yayin tattaunawa da gidan talabijin na Channels a ranar Alhamis, Bagudu ya ce jama'a ba su sauraron abinda Fulani ke fuskanta a bangare garkuwa da su ko kuma sace musu shanu.

A cikin shekarun da suka gabata, Fulani makiyaya ake zargi da kai farmaki tare da sace jama'a, lamarin da ya kawo rikicin kabilanci. Amma sai dai a koda yaushe Fulani suna cigaba da musanta cewa su ke da alhakin wannan hare-haren.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel