Da dumi-dumi: Najeriya ta yi babban rashi na wani masanin tsaro sakamakon cutar korona
- Kwararre a harkar tsaro a Najeriya kuma mai sharhi a gidan talabijin, Cif Ona Ekhomu, ya mutu
- Marubucin littafin na ‘Boko Haram: Security Considerations and the Rise of an Insurgency’ ya mutu yana da shekaru 66 a duniya
- An tattaro cewa ya mutu ne bayan ya yi fama da cutar korona
Kasar Najeriya a ranar Litinin, 9 ga watan Agusta, ta rasa daya daga cikin fitattun masana harkar tsaro, Cif Ona Ekhomu, wanda ya rubuta littafin, ‘Boko Haram: Security Considerations and the Rise of an Insurgency’.
Jaridar PM News ta ruwaito cewa Ekhomu ya mutu a ranar Litinin, 9 ga watan Agusta, a jihar Legas bayan ya yi fama da cutar COVID-19.

Shugaban na Kungiyar Tsaro da Kariya na Masana'antu na Najeriya (AISSON) ya mutu yana da shekaru 66 a duniya.
An tattaro cewa matar Ekhomu ta tuntubi abokan aikinsa a AISSON kimanin makonni biyu da suka gabata don sanar da su game da rashin lafiyarsa.
Marigayin wanda aka haife a ranar 26 ga Maris 1955 a Irrua, Jihar Edo, Najeriya, ya kasance ƙwararren masanin tsaro a Yammacin Afirka.
Jaridar ta kuma ruwaito cewa marigayin ya yi makarantar sakandare ta Western Boys, Benin City, Jihar Edo kuma ya kammala a 1972.
Bayan haka, ya samu shiga Cibiyar Nazarin Jarida ta Najeriya, Legas, 1974 kafin ya sami digiri a fanninTarihi daga Kwalejin Voorhees, Denmark.
Ya kuma sami digiri na biyu daga Jami'ar Jihar Iowa, Ames, Iowa 1979; da PhD a Harkokin Jama'a da Ƙasashen waje daga Jami'ar Pittsburgh, Amurka 1985.
Ekhomu ya halarci Makarantar Horar da Jami'in Tsaro na Allegheny County a Pennsylvania Amurka a 1986.
Ya sami lasisin Commonwealth na Pennsylvania Dokar 235 Laifin Makamai Masu Mutuka a 1986.
A wani labari na daban, Shugaban rikon kwaryan jam'iyyar All Progressives Congress, APC, a karamar hukumar Yola ta kudu, Sulaiman Adamu, ya caccaki shugaba Muhammadu Buhari, DailyNigerian ta ruwaito.

Kara karanta wannan
GMD ya yi zazzaga a NNPC, an canza wa wasu manyan ma’aikata wuraren aiki, an tsige wani
Adamu yace da so samu ne, da cutar Korona ta hallaka Buhari mataimakinsa Yemi Osinbajo ya hau kujerarsa.
Asali: Legit.ng