Nyesom Wike ya nemi alfarma wajen Gwamnatin Tarayya, Buhari ya biya masa bukatarsa

Nyesom Wike ya nemi alfarma wajen Gwamnatin Tarayya, Buhari ya biya masa bukatarsa

  • Gwamna Nyesom Wike ya ce za a gina makarantar zama Lauya a jihar Ribas
  • Nyesom Wike ya roki Gwamnatin Tarayya ta gina masa wannan makaranta
  • Gwamnatin Tarayya ta dauki wannan matakin bayan Gwamnan ya kai kuka

Mai girma Gwamna Nyesom Wike na Ribas, ya yabi matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na gina makarantar koyon aikin shari’a a jiharsa.

The Guardian ta ce Nyesom Wike ya na ganin gina wannan makaranta a Ribas duk da irin sukar da yake yi wa gwamnatin tarayya, abin a yaba ne.

Da yake magana a wajen kaddamar da fara wannan aiki a garin Rumueme a karamar hukumar Obio-Akpor, Wike ya alwashin za a karasa aikin.

KU KARANTA: Duk da ANPP ta na da Gwamnoni a 2007, Gwamna 1 ya iya taimakon Buhari

Ribas ta samu makarantar koyon aikin shari'a

Gwamna Nyesom Wike ya ce gwamnatinsa za ta dage domin ganin an gina wajen koyon ilmin shari’a a jihar Ribas wanda babu irinsa a ko ina.

Kara karanta wannan

Ortom ga Buhari: Ka daina munafurci, ka bamu 100bn tun ka ba Katsina N6.25b don kiwon zamani

Ganin gwamnatin tarayya ta amince da rokonsa, an soma ginin wannan sabuwar makaranta, Wike ya ce mutanen jihar Ribas za su samu abin yi.

“Ina mai tabbacin cewa kowa a jihar Ribas zai san cewa matakin kafa makarantar koyon ilmin shari’a a garin Fatakwal ya na da muhimmanci.”
“Ba wai kawai zai taimaka wajen ba wadanda suka karanci ilmin shari’a damar zuwa makaranta ba, zai bunkasa tattalin arziki, za a samu ayyukan yi.”

KU KARANTA: Gwamnatin Tarayya za ta ba Manoma N6.15bn a bana

Buhari
Buhari a Ribas Hoto: www.guardian.ng
Asali: UGC

AGF ya kaddamar da ginin wannan makaranta

Shugaban majalisar makarantun ilmin shari’a, Nnaemeka Ngige (SAN), ya wakilci Ministan shari’a a wajen bikin kaddamar da ginin makarantar.

A madadin Abubakar Malami, Nnaemeka Ngige, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta yarda ta gina makarantar ne bayan gwamnan ya nemi alfarma.

Ngige yake cewa duk idan za a kara gina irin wannan makaranta, dole ayi koyi da jihar Ribas.

Kara karanta wannan

Yadda na zama Alkalin mukabalar Abduljabbar Kabara da Malamai inji Salisu Shehu

Kungiyar Sarakiyya 2023 ta fito da korayen huluna a matsayin alama, suna harin kujerar Shugaban kasa. Mun samu wannan labari ne a farkon nan.

Kungiyar ta na goyon bayan Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa ya shiga Aso Rock Villa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng