Kungiyar IPOB ta kashe sojoji biyu a Enugu — Kakakin Soji

Kungiyar IPOB ta kashe sojoji biyu a Enugu — Kakakin Soji

  • An zargi bangaren tsaron kungiyar IPOB da kisan sojojin Najeriya guda biyu ranar Talata
  • Sojojin sun rasa rayukansu ne yayin musayar wuta da mayakan kungiyar IPOB
  • Ana fargabar hare-haren da kungiyar ke kai wa jami’an tsaron gwamnati sun fara dawowa

Ana zargin sashen tsaro na kungiyar IPOB (ESN), ya kashe sojoji biyu a Enugu.

A cewar Onyema Nwachukwu, kakakin rundunar, an kashe sojojin ne a ranar Talata a wani shingen binciken ababan hawa a Karamar Hukumar Uzo-Uwani na jihar, rahoton TheCable.

Ya ce mambobin kungiyar ta ESN sun yi artabu da sojojin a tsakanin su wanda ya yi sanadin mutuwar sojojin, riwayar Guardian.

Yace:

"Sojojin Najeriya da aka tura domin dakile ayyukan 'yan bindiga a garin Adani na Karamar Hukumar Uzo-Uwani a Jihar Enugu, a jiya 13 ga watan Yulin 2021, sun mayar da martanin harin da sashen tsaro na kungiyar IPOB ya kai kan sojojin a wurin binciken ababen hawa da ke Iggah/Asaba"

Kara karanta wannan

Sojojin saman Najeriya sun ragargaji 'yan ta'addan ISWAP, sun kwato makamai

“Sai dai abin takaici, a lokacin artabun da ya faru, sojoji biyu sun ce ga garinku nan. A halin yanzu sojojin suna kan bin sahun masu aika-aikar.
“Muna tabbatar wa da sauran al’umma kudurinmu na samar da isasshen tsaro a yankin baki daya tare da hadin gwiwar sauran hukumomin tsaro.

KU KARANTA: Shugaba Buhari na yiwa gwamnoninmu barazana, Jam'iyyar PDP

Kungiyar IPOB ta kashe sojoji biyu a Enugu — Kakakin Soji
Kungiyar IPOB ta kashe sojoji biyu a Enugu — Kakakin Soji
Asali: Depositphotos

DUBA NAN: Gwamnatin Buhari ba ta iya magance rashin tsaro ba - Kukah ya fada wa Amurka

A watannin baya sashen mayakan IPOB ya kaddamar da hare-hare kan cibiyoyin tsaro da kadarorin gwamnati yankin Kudu maso Gabas.

Hare-haren sun tsagaita ne bayan kama Nnamdi Kanu, shugaban kungiyar ta IPOB, inda aka tasa kyayarsa zuwa Najeriya.

Amma da alama hare-haren na neman sake kunno kai.

Jami'an tsaro na yiwa matasanmu kisan gilla, Dattawan Igbo

A bangare guda, Shugaban kungiyar dattawa Igbo, kuma tsohon Gwamnan Jihar Anambra, Cif Chukwuemeka Ezeife, ya ce matasa da dama, akasarinsu maza, ana kashe su ba bisa ka'ida ba a kowace rana daga jami'an tsaro a yankin.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Yan Ta'addan ESN-IPOB Sun Ragargaji Sojoji da Dama a Jihar Enugu

Ya bayyana hakan ne yayinda yake magana a wani taron manema labarai a Abuja, rahoton ChannelsTV.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng