Ma'aikatan SPW: Mun Kammala Biyan Akalla Mutum 400,000 Haƙkinsu Na N60,000, Keyamo

Ma'aikatan SPW: Mun Kammala Biyan Akalla Mutum 400,000 Haƙkinsu Na N60,000, Keyamo

  • Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ta kammala biyan aƙalla mutum 400,000 kuɗin su na shirin SPW
  • Ƙaramin ministan ƙwadugo, Festus Kiyamo, shine ya bayyana haka yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai
  • Yace shirin ya gunada a ƙananan hukumomi 774 da muke da su a faɗin Najeriya

Ƙaramin ministan ƙwadugo, Mr. Festus Kiyamo, yace sama da yan Najeriya 400,000 sun karɓi kuɗi Naira N60,000 na aikin SPW da gwamnatin tarayya ta ƙaddamar a shekarar 2021, kamar yadda channels tv ta ruwaito.

KARANTA ANAN: Mun Ɗauki Tsauraran Matakai Ta Yadda Ba Za'a Sake Kai Hari Makarantun Mu Ba, Gwamnatin Kaduna

Keyamo ya bayyana haka a wurin taron manema labarai a gidan gwamnati ranar Alhamis, kamar yadda vanguard ta ruwaito.

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, Keyamo yace shirin wanda aka kirkiro domin sama wa yan Najeriya aikin yi kuma a rage musu raɗaɗin da annobar korona da jefa su.

Mr. Festus Keyamo
Ma'aikatan SPW: Mun Kammala Biyan Akalla Mutum 400,000 Haƙkinsu Na N60,000, Keyamo Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

Yace yazuwa yanzun aƙalla mutum dubu N400,000 sun samu haƙƙinsu na kuɗi naira dubu N60,000.

Mr. Keyamo, yace: "A halin yanzun an rarraba Naira biliyan N24.817 ga yan Najeriya, kuma za'a duba yiwuwar ƙara mutane domin a cimma kudirin mutum 500,000 a rukunin farko."

KARANTA ANAN: Bayan Ganawa Da Buhari, Gwamna Bagudu Ya Bayyana Sunan Waɗanda Suka Sace Ɗaliban FGC Yauri

An gudanar da shirin a faɗin ƙananan hukumomi 774

Ƙaramin ministan ya ƙara jaddada cewa an gudanar da shirin a faɗin ƙananan hukumomin 774 dake Najeriya.

Ya kuma bayyana cewa shugaban ƙasa Muhammadu Buhari zai cigaba da tabbatar da an gudanar da duk shirye-shiryen da gwamnatinsa ta ƙirƙiro yadda ya kamata.

A wani labarin kuma Wasu Fusatattun Ɗalibai Sun Yi Fata-Fata da Cibiyar Zana Jarabawar JAMB CBT

Hukumar tsaro ta NSCDC ta samu nasarar damƙe wasu ɗalibai huɗu da take zargin sun lalata cibiyar rubuta jarabawa CBT a Otuoke.

Kwamandan jami'an NSCDC ta jihar Bayelsa, Mrs Christiana, ita ce ta bayyana haka ga manema labari.

Asali: Legit.ng

Online view pixel