Buhari ya sassauta, ya amince zai tattauna da 'yan kudu maso gabas kan rabewa

Buhari ya sassauta, ya amince zai tattauna da 'yan kudu maso gabas kan rabewa

  • Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da zaman tattaunawa da 'yan yankin kudu maso gabas
  • Shugaban zai yi haka ne in ji rahoto don samar da zaman lafiya a yankin na kudu maso gabas
  • A yanzu haka shugaban ya tura jami'ai da dama zuwa jihar Enugu a shirin tattaunawar dasu

Chris Ngige, Ministan kwadago, ya ce Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da karbar tattaunawa don magance rikicin dake faruwa a yankin kudu maso gabashin Najeriya.

Ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, yayin da yake zantawa da manema labarai na gidan gwamnati bayan ganawa da shugaba Muhammadu Buhari da Shugaban Ma’aikatansa, Farfesa Ibrahim Gambari, a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, The Nation ta rahoto.

A kwanakin baya kada, an yi ta kai hare-hare kan gine-ginen gwamnati a duk fadin kudu maso gabashin kasar, lamarin da ya kai ga kashe jami'an tsaro da dama.

KU KARANTA: Badakalar Tinubu: EFCC ta ce tana ci gaba da bincikar shugaban APC Tinubu

Shugaba Buhari ya sassauta, ya amince zai tattauna da 'yan IPOB
Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya da Ministan Kwadago na kasa, Chris Ngige | Hoto: wuzupnigeria.ng
Asali: UGC

Yayin da ‘yan sanda da sojoji ke zargin kungiyar tsageru ta IPOB da kitsa hare-haren, kungiyar ta sha musanta cewa tana da hannu cikin barnar, The Cable ta ruwaito.

Har ila yau, an yi ta yin korafe-korafe da barna daga sassan kudu maso gabas na nuna bukatar ballewa daga Najeriya, yayin da masu ruwa da tsaki daban-daban su ma suka koka kan yadda aka mayar da yankin saniyar ware.

Sai dai, a cewar Ngige, gwamnatin tarayya na bin wasu hanyoyin don ganin cewa mutanen kudu maso gabas ba su "ji an ware su" a Najeriya ba.

Ministan yace:

"Mun kuma kalli yanayin tsaro, musamman a shiyya ta, kudu maso gabas, kuma mun gabatar masa da wasu shawarwari bisa dogaro da son mutane, da kuma abin da gwamnatin ma ke so.
“Muna bin diddigin tattaunawa, wanda a karshe, shi ne abin da zai faru. Dole ne muyi magana; dole ne mu tattauna. Wani bangare na tattaunawar zai fara gobe.
"Ministan tsaro, ministan cikin gida, da shugabannin hafsoshi sun kasance a Enugu ranar Asabar da ta gabata kuma za mu yi taro na gaba kan hakan.

KU KARANTA: Jami'an SSS Sun Sake Cafke Wani Mawaki da Ya Zagi Annabi a Jihar Kano

Gwamnatin Buhari ta zargi gwamnonin PDP da kin kawo karshen rikicin makiyaya

A wani labarin daban, Fadar shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Laraba, ta zargi gwamnonin a karkashin jam’iyyar PDP, da kin goyon bayan kudirin kawo karshen rikicin makiyaya a kasar ta yadda za a ceci rayukan jama'a da dukiyoyinsu, BBC ta ruwaito.

Fadar shugaban kasar ta bayyana hakan ne bayan taron da kungiyar Gwamnonin PDP ta gudanar a karshen mako a Uyo babban birnin jihar Akwa Ibom a ranar Litinin.

A martaninta cikin wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar a Abuja, ya ce gwamnonin PDP ba su samar da mafita ga matsalolin kasar ba amma sun fi sha'awar abinda ya shafe su.

Asali: Legit.ng

Online view pixel