‘Muna da Ƙarfin Murƙushe Ku’, Buhari Ya Gargaɗi Ƴan Bindiga Kan Kisar Mutum 83 a Zamfara

‘Muna da Ƙarfin Murƙushe Ku’, Buhari Ya Gargaɗi Ƴan Bindiga Kan Kisar Mutum 83 a Zamfara

- Shugaba Muhammadu Buhari ya gargadi ƴan bindiga akan kisar mutane da dama a Zamfara

- Shugaban ƙasar ya ce gwamnatinsa tana da ƙarfin da za ta iya murƙushe ƴan bindigan

- Buhari ya umurci hukumomin tsaro su zage damtse domin taka wa ɓata garin birki

Shugaba Muhammadu Buhari ya gargadi ƴan bindiga cewa gwamnatinsa na da ƙarfin murƙushe su, The Cable ta ruwaito.

Buhari ya yi wannan gargaɗin ne sakamakon kashe mutane da dama da ƴan bindiga suka yi a garuruwan Zamfara.

‘Muna da Ƙarfin da Murƙushe Ku’, Buhari Ya Gargaɗi Ƴan Bindiga Kan Kisar Mutum 83 a Zamfara
‘Muna da Ƙarfin da Murƙushe Ku’, Buhari Ya Gargaɗi Ƴan Bindiga Kan Kisar Mutum 83 a Zamfara. Hoto: @thecableng
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Sunayen sabbin alƙalai 18 da Buhari ya amince da naɗinsu a kotun daukaka ƙara

Rahotanni sun nuna cewa an kashe fiye da mutum 25 a harin da aka kai a ƙananan hukumomin Gobirawa, Rini, Gora, Madoti Dankule, Bakura da Maradun a Zamfara - tuni dai adadin waɗanda aka kashe ya ƙaru.

Ƴan bindigan sun afka garuruwan a kan babur suka rika harbe-harbe a ranar Laraba.

Da ya ke martani kan batun, Buhari ya ce "dole a dakatar da kisar da aka yi wa mutanen da basu jiba ba su gani ba," ya ƙara da cewa dole a kawo karshen abin."

"Kada waɗannan ɓata-garin su yi tunanin cewa gwamnati ba za ta iya murƙushe su bane," kakakin shugaban ƙasa Garba Shehu ya ruwaito shugaban kasar ya faɗa a ranar Alhamis.

KU KARANTA: Yanzu-Yanzu: Fursunoni sunyi yunƙurin tserewa daga gidan yari a Kano

Ya ce gwamnatinsa ba za ta amince da rika cin zalin mazauna ƙauyuka da ke fama da talauci da ƙallubalen rayuwa.

Shugaban ƙasar ya umurci hukumomin tsaro su zage damtse domin ganin sun taka wa ɓata garin birki.

Buhari ya bawa mazauna jihar tabbacin cewa gwamnatinsa za ta yi duk mai yiwuwa domin cin galaba kan maƙiya duk da wannan koma bayan da aka samu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164