Sunayen sabbin alƙalai 18 da Buhari ya amince da naɗinsu a kotun daukaka ƙara

Sunayen sabbin alƙalai 18 da Buhari ya amince da naɗinsu a kotun daukaka ƙara

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin sabbin alkalai 18 na kotunan daukaka kara a Nigeria, The Cable ta ruwaito.

Kwamitin Kolin Shari'a ta Kasa, NJC, Karkashin jagorancin Ibrahim Muhammad, Alkalin Alkalan Nigeria, CJN, a watan Maris ya mika sunayensu ga shugaban kasa domin a musu karin girma.

Jerin Sunaye: Buhari ya amince da naɗin alƙalai 18 na kotun ɗaukaka ƙara
Jerin Sunaye: Buhari ya amince da naɗin alƙalai 18 na kotun ɗaukaka ƙara. Hoto: @thecableng
Asali: Twitter

A cikin wasikar da ya aike wa CJN din, Farfesa Ibrahim Gambari, Shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, ya ce Buhari ya amince da bukatar yi wa alkalan karin girma.

DUBA WANNAN: Maigida ta nemi na kwanta da ita a madadin biyan kuɗin haya, in ji Saurayi

"Ina farin cikin sanar da kai cewa Mai girma Shugaban kasa ya amince da nadin wadannan a matsayin alkalan kotun daukaka kara saboda matayinsu a kotun kamar yadda ya ke a sashi na 237 da 238 na kundin tsarin mulkin 1999," a cewar wasikar.

Shugaban kasar ya kuma yi wa sabbin alkalan da aka nada fatan alheri a yayin da za su cigaba da ayyukansu a kotunan daukaka kara.

Ga jerin sunayen alkalan:

KU KARANTA: Kotun shari'a ta raba aure a Zamfara saboda tsabar girman mazakutar miji

  1. Bature Isah Gafai
  2. Muhammad Ibrahim Sirajo
  3. Waziri Abdul-Azeez
  4. Yusuf Alhaji Bashir
  5. Usman A. Musale
  6. Jauro Ibrahim Wakili
  7. Abba Bello Mohammed
  8. Mohammed Danjuma
  9. Danlami Zama Senchi
  10. Mohammed Lawal Abubakar
  11. Hassan Muslim Sule
  12. Amadi Kenneth Ikechukwu
  13. Peter Oyinkenimiemi Affen
  14. Sybil Onyeji Nwaka Gbagi
  15. Olasumbo Olanrewaju Goodluck
  16. Banjoko Adebukunola Adeoti Ibironke
  17. Olabode Abimbola Adegbehingbe
  18. Bola Samuel Ademola

A wani labarin daban kun ji cewa 'yan sanda a jihar Kano sun ceto wata yarinya mai shekaru 15, Aisha Jibrin, da iyayenta suka kulle ta a daki tsawon shekaru 10 a Darerewa Quaters a karamar hukumar Fagge ta jihar Kano.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan Kano, Abdullahi Kiyawa cikin sanarwar da ya fitar a ranar Talata ya ce mahaifiyarta Rabi Muhammad tana hannunsu amma mahaifinta ya tsere.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan Kano, Abdullahi Kiyawa cikin sanarwar da ya fitar a ranar Talata ya ce mahaifiyarta Rabi Muhammad tana hannunsu amma mahaifinta ya tsere.

Asali: Legit.ng

Online view pixel