Da duminsa: 'Yan bindiga sun yi awon gaba da shugaban karamar hukuma a Ribas

Da duminsa: 'Yan bindiga sun yi awon gaba da shugaban karamar hukuma a Ribas

- Miyagun 'yan bindiga sun kai farmaki inda suka sace shugaban karamar hukumar Okrika na jihar Ribas

- Lamarin ya auku ne a titin Peter Odili inda 'yan bindiga suka yi awon gaba da Honarabul Philemon Kingoli

- A wannan daren ne wasu 'yan bindiga da ake zargin 'yan kungiyar asiri ne suka kai farmaki wani otal a Fatakwal

Wasu 'yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun sace shugaban karamar hukumar Okrika dake jihar Ribas, Honarabul Philemon Kingoli, a Fatakwal.

Wannan lamarin ya faru ne bayan an harbe tare da kashe wasu 'yan bindiga da ake zargin 'yan kungiyar asiri ne a wani otal dake Fatakwal.

Leadership ta tattaro cewa, Kingoli wanda cikin kwanakin nan ya rasa damar hayewa kujerarsa a karo na biyu karkashin jam'iyyar PDP, an sace shi ne a kan titin Peter Odili dake Fatakwal.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, Nnamdi Omoni, har yanzu bai riga ya tabbatar da aukuwar lamarin ba.

KU KARANTA: Sojin Najeriya sun mamaye garinsu ministan Buhari, suna zuba ruwan wuta

Da duminsa: 'Yan bindiga sun yi awon gaba da shugaban karamar hukuma a Ribas
Da duminsa: 'Yan bindiga sun yi awon gaba da shugaban karamar hukuma a Ribas. Hoto daga @Leadership
Asali: Twitter

KU KARANTA: Hotunan Zulum yana gwangwaje 'yan gudun hijira da N200m da kayan abinci a Bama

Har ila yau, an kashe mutum biyu a ranar Laraba yayin da wasu suka samu raunika yayin da 'yan bindigan da ake zargin 'yan kungiyar asiri ne suka kai farmaki wani otal dake kan titin Victoria a Fatakwal.

Wannan cigaban ya kawo tsananin tsoro da tashin hankali ga mazauna tsohon birnin Fatakwal wanda hakan yasa wasu suka fara gudu don ceton rayukansu.

A halin yanzu, rundunar 'yan sandan jihar ta tura wasu 'yan sanda yankin domin tabbatar da doka da oda.

A wani labari na daban, sabon sifeta janar na 'yan sanda, Usman Alkali ya ce 'yan sanda a karkashin mulkinsa zasu tabbatar da bunkasa harkar tsaro a Najeriya.

Ya kara da bada tabbacin fifitawa da kuma tabbatar da 'yan sandan jihohi a karkashin mulkinsa.

IGP ya bayyana hakan ne a gidan gwamnati dake Abuja bayan mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya nada shi.

Shugaba Muhammadu Buhari ya daura Alkali a kujerar sifeta janar na 'yan sandan Najeriya, inda ya maye gurbin Mohammed Adamu wanda ya kamata ya sauka daga madafin iko a watan Fabrairu, saidai an kara masa watanni 3.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel